< Karin Magana 2 >
1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Hai anakku, jikalau engkau menerima perkataanku dan menyimpan perintahku di dalam hatimu,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
sehingga telingamu memperhatikan hikmat, dan engkau mencenderungkan hatimu kepada kepandaian,
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
ya, jikalau engkau berseru kepada pengertian, dan menujukan suaramu kepada kepandaian,
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
jikalau engkau mencarinya seperti mencari perak, dan mengejarnya seperti mengejar harta terpendam,
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
maka engkau akan memperoleh pengertian tentang takut akan TUHAN dan mendapat pengenalan akan Allah.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Karena Tuhanlah yang memberikan hikmat, dari mulut-Nya datang pengetahuan dan kepandaian.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Ia menyediakan pertolongan bagi orang yang jujur, menjadi perisai bagi orang yang tidak bercela lakunya,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
sambil menjaga jalan keadilan, dan memelihara jalan orang-orang-Nya yang setia.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Maka engkau akan mengerti tentang kebenaran, keadilan, dan kejujuran, bahkan setiap jalan yang baik.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Karena hikmat akan masuk ke dalam hatimu dan pengetahuan akan menyenangkan jiwamu;
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
kebijaksanaan akan memelihara engkau, kepandaian akan menjaga engkau
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
supaya engkau terlepas dari jalan yang jahat, dari orang yang mengucapkan tipu muslihat,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
dari mereka yang meninggalkan jalan yang lurus dan menempuh jalan yang gelap;
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
yang bersukacita melakukan kejahatan, bersorak-sorak karena tipu muslihat yang jahat,
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
yang berliku-liku jalannya dan yang sesat perilakunya;
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
supaya engkau terlepas dari perempuan jalang, dari perempuan yang asing, yang licin perkataannya,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
yang meninggalkan teman hidup masa mudanya dan melupakan perjanjian Allahnya;
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
sesungguhnya rumahnya hilang tenggelam ke dalam maut, jalannya menuju ke arwah-arwah.
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Segala orang yang datang kepadanya tidak balik kembali, dan tidak mencapai jalan kehidupan.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Sebab itu tempuhlah jalan orang baik, dan peliharalah jalan-jalan orang benar.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Karena orang jujurlah akan mendiami tanah, dan orang yang tak bercelalah yang akan tetap tinggal di situ,
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
tetapi orang fasik akan dipunahkan dari tanah itu, dan pengkhianat akan dibuang dari situ.