< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Mein Sohn, wenn du meine Lehren annimmst und meine Weisungen bei dir verwahrst,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
indem du dein Ohr auf Weisheit lauschen läßt und dein Herz der Einsicht zuwendest,
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
ja, wenn du nach der Verständigkeit rufst und deine Stimme laut nach der Einsicht erschallen läßt,
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
wenn du nach ihr suchst wie nach Silber und ihr nachspürst wie verborgenen Schätzen:
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
dann wirst du die Furcht vor dem HERRN verstehen lernen und die Erkenntnis Gottes gewinnen –
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
denn der HERR ist’s, der Weisheit verleiht: aus seinem Munde kommt Erkenntnis und Einsicht;
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
er hält für die Rechtschaffenen Glück in Bereitschaft und ist ein Schild für die, welche unsträflich wandeln,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
indem er die Pfade des Rechts behütet und über dem Ergehen seiner Frommen wacht –;
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
dann wirst du Verständnis gewinnen für Gerechtigkeit und Recht, für Rechtschaffenheit (und überhaupt) für jegliche Bahn des Guten.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Denn Weisheit wird in dein Herz einziehen und Erkenntnis deiner Seele erfreulich sein;
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
Besonnenheit wird über dich wachen und Einsicht dich behüten,
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
indem sie dich vor dem Wege der Bösen bewahrt, vor den Menschen, die Verkehrtes reden,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
vor denen, welche die geraden Pfade verlassen, um auf den Wegen der Finsternis zu wandeln;
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
die ihre Freude daran haben, Böses zu verüben, und über boshafte Verkehrtheit frohlocken;
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
deren Pfade krumm sind und die in ihren Bahnen auf Abwege geraten –;
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
indem sie dich vom Eheweibe eines anderen fernhält, von der fremden Frau, die glatte Reden führt,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
die den trauten Freund ihrer Jugend verlassen und den vor ihrem Gott geschlossenen Ehebund vergessen hat;
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
denn zum Tode sinkt ihr Pfad hinab, und zum Schattenreich (führen) ihre Bahnen;
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
keiner von denen, die zu ihr eingehen, kehrt zurück, und keiner erreicht die Pfade des Lebens –;
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
damit du auf dem Wege der Guten wandelst und die Pfade der Gerechten einhältst.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Denn die Rechtschaffenen werden das Land bewohnen und die Unsträflichen darin übrigbleiben;
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
die Gottlosen aber werden aus dem Lande ausgerottet und die Treulosen aus ihm entwurzelt.

< Karin Magana 2 >