< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Mon fils, si tu reçois mes paroles, Et si tu gardes avec toi mes préceptes,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
Si tu rends ton oreille attentive à la sagesse, Et si tu inclines ton cœur à l’intelligence;
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
Oui, si tu appelles la sagesse, Et si tu élèves ta voix vers l’intelligence,
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
Si tu la cherches comme l’argent, Si tu la poursuis comme un trésor,
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
Alors tu comprendras la crainte de l’Éternel, Et tu trouveras la connaissance de Dieu.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Car l’Éternel donne la sagesse; De sa bouche sortent la connaissance et l’intelligence;
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Il tient en réserve le salut pour les hommes droits, Un bouclier pour ceux qui marchent dans l’intégrité,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
En protégeant les sentiers de la justice Et en gardant la voie de ses fidèles.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Alors tu comprendras la justice, l’équité, La droiture, toutes les routes qui mènent au bien.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Car la sagesse viendra dans ton cœur, Et la connaissance fera les délices de ton âme;
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
La réflexion veillera sur toi, L’intelligence te gardera,
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
Pour te délivrer de la voie du mal, De l’homme qui tient des discours pervers,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
De ceux qui abandonnent les sentiers de la droiture Afin de marcher dans des chemins ténébreux,
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
Qui trouvent de la jouissance à faire le mal, Qui mettent leur plaisir dans la perversité,
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
Qui suivent des sentiers détournés, Et qui prennent des routes tortueuses;
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
Pour te délivrer de la femme étrangère, De l’étrangère qui emploie des paroles doucereuses,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
Qui abandonne l’ami de sa jeunesse, Et qui oublie l’alliance de son Dieu;
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
Car sa maison penche vers la mort, Et sa route mène chez les morts:
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Aucun de ceux qui vont à elle ne revient, Et ne retrouve les sentiers de la vie.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Tu marcheras ainsi dans la voie des gens de bien, Tu garderas les sentiers des justes.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Car les hommes droits habiteront le pays, Les hommes intègres y resteront;
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
Mais les méchants seront retranchés du pays, Les infidèles en seront arrachés.

< Karin Magana 2 >