< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Mon fils, si tu reçois mes paroles et que tu caches par-devers toi mes commandements
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
pour rendre ton oreille attentive à la sagesse, si tu inclines ton cœur à l’intelligence,
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
si tu appelles le discernement, si tu adresses ta voix à l’intelligence,
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
si tu la cherches comme de l’argent et que tu la recherches comme des trésors cachés,
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
alors tu comprendras la crainte de l’Éternel et tu trouveras la connaissance de Dieu.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Car l’Éternel donne la sagesse; de sa bouche [procèdent] la connaissance et l’intelligence:
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
il réserve de sains conseils pour les hommes droits; il est un bouclier pour ceux qui marchent dans l’intégrité,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
protégeant les sentiers de juste jugement et gardant la voie de ses saints.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Alors tu discerneras la justice et le juste jugement et la droiture, toute bonne voie.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Si la sagesse entre dans ton cœur et si la connaissance est agréable à ton âme,
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
la réflexion te préservera, l’intelligence te protégera:
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
Pour te sauver du mauvais chemin, de l’homme qui prononce des choses perverses,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
[de ceux] qui abandonnent les sentiers de la droiture pour marcher dans les voies de ténèbres,
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
qui se réjouissent à mal faire, qui s’égaient en la perversité du mal,
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
dont les sentiers sont tortueux et qui s’égarent dans leurs voies;
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
Pour te sauver de la femme étrangère, de l’étrangère qui use de paroles flatteuses,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
qui abandonne le guide de sa jeunesse, et qui a oublié l’alliance de son Dieu;
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
– car sa maison penche vers la mort, et ses chemins vers les trépassés:
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
aucun de ceux qui entrent auprès d’elle ne revient ni n’atteint les sentiers de la vie;
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
– afin que tu marches dans la voie des gens de bien, et que tu gardes les sentiers des justes.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Car les hommes droits habiteront le pays, et les hommes intègres y demeureront de reste;
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
mais les méchants seront retranchés du pays, et les perfides en seront arrachés.

< Karin Magana 2 >