< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
My son, if thou wilt receive my words, and lay up my commandments with thee;
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
So that thou make thine ear attend unto wisdom, and thy heart incline to discernment;
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
Yea, if thou call for understanding, and lift up thy voice for discernment;
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
If thou seek her as silver, and search for her as for hid treasures;
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
Then shalt thou understand the fear of the LORD, and find the knowledge of God.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
For the LORD giveth wisdom, out of His mouth cometh knowledge and discernment;
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
He layeth up sound wisdom for the upright, He is a shield to them that walk in integrity;
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
That He may guard the paths of justice, and preserve the way of His godly ones.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Then shalt thou understand righteousness and justice, and equity, yea, every good path.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
For wisdom shall enter into thy heart, and knowledge shall be pleasant unto thy soul;
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
Discretion shall watch over thee, discernment shall guard thee;
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
To deliver thee from the way of evil, from the men that speak froward things;
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
Who leave the paths of uprightness, to walk in the ways of darkness;
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
Who rejoice to do evil, and delight in the frowardness of evil;
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
Who are crooked in their ways, and perverse in their paths;
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
To deliver thee from the strange woman, even from the alien woman that maketh smooth her words;
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
That forsaketh the lord of her youth, and forgetteth the covenant of her God.
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
For her house sinketh down unto death, and her paths unto the shades;
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
None that go unto her return, neither do they attain unto the paths of life;
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
That thou mayest walk in the way of good men, and keep the paths of the righteous.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
For the upright shall dwell in the land, and the whole-hearted shall remain in it.
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
But the wicked shall be cut off from the land, and the faithless shall be plucked up out of it.

< Karin Magana 2 >