< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Min Søn! dersom du vil tage imod mine Ord og gemme mine Rud hos dig,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
saa at du lader dit Øre give Agt paa Visdommen, bøjer dit Hjerte til Indsigt;
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
ja, dersom du kalder paa Forstanden, opløfter din Røst efter Indsigt;
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
dersom du søger efter den som efter Sølv og ransager efter den som efter skjulte Skatte:
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
Da skal du forstaa Herrens Frygt og finde Guds Kundskab.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Thi Herren giver Visdom, af hans Mund er Kundskab og Indsigt.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Han gemmer det varige gode til de oprigtige; han er et Skjold for dem, som vandre fuldkommelig,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
saa han bevogter Rettens Stier og bevarer sine helliges Vej.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Da skal du forstaa Ret og Retfærdighed og Retvished, al god Vej.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Thi Visdom skal komme i dit Hjerte og Kundskab være liflig for din Sjæl.
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
Kløgt skal bevare dig og Indsigt bevogte dig
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
for at fri dig fra Ondskabs Vej, fra en Mand, som taler forvendte Ting;
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
fra dem, som forlade Rettens Stier for at gaa paa Mørkets Veje;
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
dem, som glæde sig ved at gøre ondt og fryde sig i Ondskabs Forvendthed;
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
dem, hvis Stier ere krogede, og hvis Veje ere bugtede;
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
for at fri dig fra en fremmed Kvinde, fra en ubekendt, som gør sine Ord glatte,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
hende, som har forladt sin Ungdoms Ven, og som har glemt sin Guds Pagt;
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
thi hendes Hus bøjer ned imod Døden og hendes Veje til Dødningerne;
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
alle de, som gaa ind til hende, skulle ikke komme tilbage og ikke naa Livsens Stier; —
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
paa det du kan vandre paa de godes Vej og holde dig paa de retfærdiges Stier.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Thi de retskafne skulle bo i Landet og de oprigtige blive tilovers derudi;
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
men de ugudelige skulle udryddes af Landet og de troløse udslettes deraf.

< Karin Magana 2 >