< Karin Magana 19 >
1 Gara matalauci wanda yake marar laifi da wawa wanda leɓunansa masu ƙarya ne.
Better is the poor who walks in his simplicity, than the rich who twists his lips and is unwise.
2 Ba shi da kyau ka kasance da niyya babu sani, ko ka kasance mai garaje ka ɓace hanya.
Where there is no knowledge of the soul, there is no good. And whoever hurries with his feet will stumble.
3 Wautar mutum kan lalatar da ransa, duk da haka zuciyarsa kan ba wa Ubangiji laifi.
The foolishness of a man undermines his steps. And then he seethes in his soul against God.
4 Wadata kan kawo abokai da yawa, amma abokin matalauci kan bar shi.
Riches add many friends. But from the pauper, even those whom he had become separated.
5 Mai ba da shaidar ƙarya ba zai tafi babu hukunci ba, kuma duk wanda ya baza ƙarairayi ba zai kuɓuta ba.
A false witness shall not go unpunished. And whoever speaks lies will not escape.
6 Kowa na ƙoƙari ya sami farin jini wurin mai mulki, kuma kowa na so a ce shi abokin mutumin nan mai yawan kyauta ne.
Many honor the character of one who is powerful, and there are friends for a giver of gifts.
7 ’Yan’uwan matalauci sukan guje shi, balle abokansa, su ma za su guje shi. Ko da yake matalaucin yana binsu yana roƙo, ba zai sam su ba.
The brothers of the poor man hate him. Moreover, even his friends have withdrawn far from him. Whoever pursues only words shall have nothing.
8 Duk wanda ya sami hikima yana ƙaunar ransa; duka wanda yake jin daɗi fahimi kan ci gaba.
But whoever possesses reason loves his own soul. And one who guards prudence shall discover good things.
9 Mai shaidar ƙarya ba zai tafi babu hukunci ba, kuma duk mai baza ƙarairayi zai hallaka.
A false witness shall not go unpunished. And whoever speaks lies will perish.
10 Bai dace da wawa ya yi rayuwa cikin jin daɗi ba, haka ya fi muni bawa ya yi mulki a kan sarki!
Fine things are not fitting for the foolish, nor is it fitting for a servant to rule over princes.
11 Hikimar mutum kan ba shi haƙuri; ɗaukakarsa ce ya ƙyale laifi.
The doctrine of a man is known through patience. And his glory is to pass beyond iniquities.
12 Fushin sarki yana kama da rurin zaki, amma tagomashinsa yana kama da raba a kan ciyawa.
Like the roaring of a lion, so also is the wrath of a king. And his cheerfulness is like the dew upon the grass.
13 Wawan yaro lalacin mahaifinsa ne, mace mai yawan faɗa tana kama da ɗiɗɗigar ruwa.
A foolish son is the grief of his father. And an argumentative wife is like a roof that is continually leaking.
14 Ana gādon dawakai da wadata daga iyaye ne, amma mace mai basira daga Ubangiji ne.
A house and its riches are given by parents. But a prudent wife is particularly from the Lord.
15 Ragwanci kan jawo zurfin barci, mutum mai sanyin jiki kuma yana tare da yunwa.
Laziness sends one into a deep sleep, and a dissolute soul will go hungry.
16 Duk wanda ya bi umarnai kan tsare ransa, amma duk wanda ya ƙi binsu zai mutu.
Whoever guards a commandment guards his own soul. But whoever neglects his own way will die.
17 Duk wanda yake kirki ga matalauta yana ba wa Ubangiji bashi ne, zai kuwa sami lada game da abin da ya yi.
Whoever is merciful to the poor lends to the Lord. And he will repay him for his efforts.
18 Ka hori ɗanka, gama yin haka akwai sa zuciya; kada ka goyi baya lalacewarsa.
Teach your son; do not despair. But do not set your soul toward putting him to death.
19 Dole mai zafin rai yă biya tara; in ka fisshe shi sau ɗaya, to, sai ka sāke yin haka.
Whoever is impatient will sustain damage. And when it has been taken away, he will set up another.
20 Ka kasa kunne ga shawara ka kuma yarda da umarni, a ƙarshe kuwa za ka yi hikima.
Listen to counsel and take up discipline, so that you may be wise in your latter days.
21 Da yawa ne shirye-shiryen zuciyar mutum, amma manufar Ubangiji ce takan cika.
There are many intentions in the heart of a man. But the will of the Lord shall stand firm.
22 Abin da mutum yake sha’awa shi ne ƙauna marar ƙarewa; gara ka zama matalauci da ka zama maƙaryaci.
An indigent man is merciful. And a pauper is better than a deceitful man.
23 Tsoron Ubangiji yakan kai ga rai. Sa’an nan mutum ya sami biyan bukata, ba abin da zai cuce shi.
The fear of the Lord is unto life. And he shall linger in plentitude, without being visited by disaster.
24 Rago kan sa hannunsa a kwano ba ya ma iya ɗaga shi ya kai bakinsa!
The lazy conceals his hand under his arm, and he will not so much as bring it to his mouth.
25 Ka bulale mai ba’a, marasa azanci kuwa za su yi la’akari; ka tsawata wa mai basira, zai kuwa ƙara sani.
When the pestilent are scourged, the foolish will become wiser. But if you chastise the wise, he will understand discipline.
26 Duk wanda ya yi wa mahaifinsa fashi ya kuma kori mahaifiyarsa ɗa ne da kan kawo kunya da wulaƙanci.
Whoever afflicts his father and flees from his mother is disreputable and unhappy.
27 In ka daina jin umarni, ɗana, za ka kuwa kauce daga kalmomin sani.
Son, do not cease listening to doctrine, and do not be ignorant of the sermons of knowledge.
28 Mai shaidar da yake malalaci yana wa shari’a ba’a ne, bakin mugaye kuma na haɗiye mugunta.
An unjust witness ridicules judgment. And the mouth of the impious devours iniquity.
29 An shirya tara saboda masu ba’a ne, dūka kuma saboda bayan wawaye.
Judgments are prepared for those who ridicule. And striking hammers are prepared for the bodies of the foolish.