< Karin Magana 18 >
1 Mutumin da ba ya abokantaka yakan nema ya cika burinsa ne kaɗai; yakan ƙi yarda da kowace maganar da take daidai.
Człowiek swej myśli, szuka tego, co mu się podoba, a w każdą rzecz wtrąca się.
2 Wawa ba ya sha’awa ya sami fahimta amma abin da yake so ya yi kaɗai, shi ne ya ba da ra’ayinsa.
Nie kocha się głupi w roztropności, ale w tem, co mu objawia serce jego.
3 Sa’ad da mugunci ya zo, reni ma kan zo, haka kuma sa’ad da kunya ta zo, shan kunya kan biyo.
Gdy przychodzi niezbożny, przychodzi też wzgarda, a z mężem lekkomyślnym urąganie.
4 Kalmomin bakin mutum suna da zurfi kamar ruwaye, amma maɓulɓulan hikima rafi ne mai gudu.
Słowa ust męża mądrego są jako wody głębokie, a źródło mądrości jako potok wylewający.
5 Ba shi da kyau ka yi wa mugu alheri ko ka hana wa marar laifi adalci.
Nie dobra to, mieć wzgląd na osobę niezbożnego, aby był podwrócony sprawiedliwy w sądzie.
6 Leɓunan wawa kan jawo masa faɗa, bakinsa kuma kan gayyaci dūka.
Wargi głupiego zmierzają do swaru, a usta jego do bitwy wyzywają.
7 Bakin wawa lalatar da kansa yake yi leɓunansa kuma tarko ne ga ransa.
Usta głupiego są upadkiem jego, a wargi jego sidłem duszy jego.
8 Kalmomin mai gulma kamar abinci mai daɗi suke; sukan gangara zuwa can cikin gaɓoɓin mutum.
Słowa obmówcy są jako słowa zranionych, a wszakże przenikają do wnętrzności żywota.
9 Wanda yake ragwanci a aikinsa ɗan’uwa ne ga wanda yakan lalatar da abubuwa.
Kto niedbały w sprawach swoich, bratem jest utratnika.
10 Sunan Ubangiji hasumiya ce mai ƙarfi; masu adalci kan gudu zuwa wurinta don su zauna lafiya.
Imię Pańskie jest mocną wieżą; sprawiedliwy się do niej uciecze, a wywyższony będzie.
11 Dukiyar masu arziki ita ce birninsu mai katanga; suna gani cewa ba za a iya huda katangar ba.
Majętność bogatego jest miastem jego mocnem, a jako mur wysoki w myśli jego.
12 Kafin fāɗuwarsa zuciyar mutum takan yi girman kai, amma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.
Przed upadkiem podnosi się serce człowiecze, a sławę uprzedza poniżenie.
13 Duk wanda yakan ba da amsa kafin ya saurara, wannan wauta ce da kuma abin kunya.
Kto odpowiada, pierwej niż wysłucha, głupstwo to jego i zelżywość.
14 Sa rai da mutum ke yi kan taimake shi sa’ad da yake ciwo, amma in ya karai, to, tasa ta ƙare.
Duch męża znosi niemoc swoję; ale ducha utrapionego któż zniesie?
15 Zuciya mai la’akari kan nemi sani; kunnuwan mai hikima kan bincika don yă koya.
Serce rozumne nabywa umiejętności, a ucho mądrych szuka jej.
16 Kyauta kan buɗe hanya wa mai bayarwa yakan kuma kai shi a gaban babban mutum.
Dar człowieczy plac mu czyni, i przed wielmożnych przywodzi go.
17 Wanda ya fara mai da jawabi yakan zama kamar shi ne mai gaskiya, sai wani ya fito ya yi masa tambaya tukuna.
Sprawiedliwym zda się ten, kto pierwszy w sprawie swojej; ale gdy przychodzi bliźni jego, dochodzi go.
18 Jefa ƙuri’a kan daidaita tsakanin masu faɗa ta kuma ajiye masu faɗan a rabe.
Los uśmierza zwady, i między możnymi rozsądek czyni.
19 Ɗan’uwan da aka yi wa laifi ya fi birni mai katanga wuyan shiryawa, kuma faɗace-faɗace suna kama da ƙofofin ƙarfe na fada.
Brat krzywdą urażony trudniejszy nad miasto niedobyte, a swary są jako zawory u pałacu.
20 Daga abin da baki ya furta ne cikin mutum kan cika; girbi daga leɓunansa kuma yakan ƙoshi.
Z owocu ust każdego nasycon bywa żywot jego; urodzajem warg swych będzie nasycony.
21 Harshe yana da ikon rai da mutuwa, kuma waɗanda suke ƙaunarsa za su ci amfaninsa.
Śmierć i żywot jest w mocy języka, a kto go miłuje, będzie jadł owoce jego.
22 Duk wanda ya sami mace ya sami abu mai kyau ya kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Kto znalazł żonę, znalazł rzecz dobrą, i dostąpił łaski od Pana.
23 Matalauci kan yi roƙo da taushi, amma mawadaci kan amsa da kakkausar murya.
Ubogi pokornie mówi; ale bogaty odpowiada surowie.
24 Mutum mai abokai masu yawa kan lalace, amma akwai abokin da yakan manne kurkusa fiye da ɗan’uwa.
Człowiek, który ma przyjaciół, ma się obchodzić po przyjacielsku, ponieważ przyjaciel bywa przychylniejszy nad brata.