< Karin Magana 18 >

1 Mutumin da ba ya abokantaka yakan nema ya cika burinsa ne kaɗai; yakan ƙi yarda da kowace maganar da take daidai.
Celui qui veut rompre avec son ami en cherche les occasions; mais il sera couvert d’opprobre en tout temps.
2 Wawa ba ya sha’awa ya sami fahimta amma abin da yake so ya yi kaɗai, shi ne ya ba da ra’ayinsa.
L’insensé ne reçoit pas les paroles de la prudence, à moins que tu ne lui dises les choses qui se trouvent dans son cœur.
3 Sa’ad da mugunci ya zo, reni ma kan zo, haka kuma sa’ad da kunya ta zo, shan kunya kan biyo.
L’impie, lorsqu’il est venu au fond des péchés, méprise; mais l’ignominie le suit ainsi que l’opprobre.
4 Kalmomin bakin mutum suna da zurfi kamar ruwaye, amma maɓulɓulan hikima rafi ne mai gudu.
C’est une eau profonde que les paroles qui sortent de la bouche de l’homme, et un torrent débordé que la source de la sagesse.
5 Ba shi da kyau ka yi wa mugu alheri ko ka hana wa marar laifi adalci.
Faire acception de la personne d’un impie n’est pas une bonne chose, pour que tu t’écartes de la vérité dans le jugement.
6 Leɓunan wawa kan jawo masa faɗa, bakinsa kuma kan gayyaci dūka.
Les lèvres de l’insensé se mêlent dans des rixes, et sa bouche provoque des querelles.
7 Bakin wawa lalatar da kansa yake yi leɓunansa kuma tarko ne ga ransa.
La bouche de l’insensé est sa destruction; et ses lèvres sont la ruine de son âme.
8 Kalmomin mai gulma kamar abinci mai daɗi suke; sukan gangara zuwa can cikin gaɓoɓin mutum.
Les paroles d’un homme à double langue paraissent simples; et elles pénètrent jusqu’au fond des entrailles. La crainte abat le paresseux; mais les âmes des efféminés auront faim.
9 Wanda yake ragwanci a aikinsa ɗan’uwa ne ga wanda yakan lalatar da abubuwa.
Celui qui est mou et lâche dans son ouvrage est frère de celui qui détruit les ouvrages.
10 Sunan Ubangiji hasumiya ce mai ƙarfi; masu adalci kan gudu zuwa wurinta don su zauna lafiya.
C’est une tour très forte que le nom du Seigneur; le juste y court, et il sera exalté.
11 Dukiyar masu arziki ita ce birninsu mai katanga; suna gani cewa ba za a iya huda katangar ba.
Le bien du riche est sa ville forte, et comme une muraille solide qui l’environne.
12 Kafin fāɗuwarsa zuciyar mutum takan yi girman kai, amma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.
Avant qu’il soit brisé, le cœur de l’homme est exalté; et avant d’être élevé en gloire, il est humilié.
13 Duk wanda yakan ba da amsa kafin ya saurara, wannan wauta ce da kuma abin kunya.
Celui qui répond avant d’écouter se montre insensé et digne de confusion.
14 Sa rai da mutum ke yi kan taimake shi sa’ad da yake ciwo, amma in ya karai, to, tasa ta ƙare.
L’esprit de l’homme soutient sa faiblesse; mais un esprit facile à se mettre en colère, qui pourra le soutenir?
15 Zuciya mai la’akari kan nemi sani; kunnuwan mai hikima kan bincika don yă koya.
Le cœur prudent possédera la science; et l’oreille des sages cherche la doctrine.
16 Kyauta kan buɗe hanya wa mai bayarwa yakan kuma kai shi a gaban babban mutum.
Le présent d’un homme élargit sa voie, et devant les princes lui fait faire place.
17 Wanda ya fara mai da jawabi yakan zama kamar shi ne mai gaskiya, sai wani ya fito ya yi masa tambaya tukuna.
Le juste est le premier accusateur de lui-même; vient son ami, et il l’examinera.
18 Jefa ƙuri’a kan daidaita tsakanin masu faɗa ta kuma ajiye masu faɗan a rabe.
Le sort apaise les différends; et entre les puissants mêmes, il sert d’arbitre.
19 Ɗan’uwan da aka yi wa laifi ya fi birni mai katanga wuyan shiryawa, kuma faɗace-faɗace suna kama da ƙofofin ƙarfe na fada.
Un frère qui est aidé par son frère est comme une cité forte; et leurs jugements sont comme les verrous des portes des villes.
20 Daga abin da baki ya furta ne cikin mutum kan cika; girbi daga leɓunansa kuma yakan ƙoshi.
Le ventre de l’homme sera rempli du fruit de sa bouche; et les produits de ses lèvres le rassasieront.
21 Harshe yana da ikon rai da mutuwa, kuma waɗanda suke ƙaunarsa za su ci amfaninsa.
La mort et la vie sont au pouvoir de la langue; ceux qui l’aiment mangeront ses fruits.
22 Duk wanda ya sami mace ya sami abu mai kyau ya kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Celui qui a trouvé une femme vertueuse a trouvé un bien; et il puisera la joie dans le Seigneur. Celui qui chasse une femme vertueuse rejette un bien; mais celui qui retient une adultère est insensé et impie.
23 Matalauci kan yi roƙo da taushi, amma mawadaci kan amsa da kakkausar murya.
C’est avec des supplications que parlera le pauvre; mais le riche s’énoncera sévèrement.
24 Mutum mai abokai masu yawa kan lalace, amma akwai abokin da yakan manne kurkusa fiye da ɗan’uwa.
L’homme aimable à la société sera plus ami qu’un frère.

< Karin Magana 18 >