< Karin Magana 18 >

1 Mutumin da ba ya abokantaka yakan nema ya cika burinsa ne kaɗai; yakan ƙi yarda da kowace maganar da take daidai.
A man who wishes to separate from friends seeks excuses; but at all times he will be liable to reproach.
2 Wawa ba ya sha’awa ya sami fahimta amma abin da yake so ya yi kaɗai, shi ne ya ba da ra’ayinsa.
A senseless man feels no need of wisdom, for he is rather led by folly.
3 Sa’ad da mugunci ya zo, reni ma kan zo, haka kuma sa’ad da kunya ta zo, shan kunya kan biyo.
When an ungodly man comes into a depth of evils, he despises [them]; but dishonour and reproach come upon him.
4 Kalmomin bakin mutum suna da zurfi kamar ruwaye, amma maɓulɓulan hikima rafi ne mai gudu.
A word in the heart of a man is a deep water, and a river and fountain of life spring forth.
5 Ba shi da kyau ka yi wa mugu alheri ko ka hana wa marar laifi adalci.
[It is] not good to accept the person of the ungodly, nor [is it] holy to pervert justice in judgment.
6 Leɓunan wawa kan jawo masa faɗa, bakinsa kuma kan gayyaci dūka.
The lips of a fool bring [him] into troubles, and his bold mouth calls for death.
7 Bakin wawa lalatar da kansa yake yi leɓunansa kuma tarko ne ga ransa.
A fool's mouth is ruin to him, and his lips are a snare to his soul.
8 Kalmomin mai gulma kamar abinci mai daɗi suke; sukan gangara zuwa can cikin gaɓoɓin mutum.
Fear casts down the slothful; and the souls of the effeminate shall hunger.
9 Wanda yake ragwanci a aikinsa ɗan’uwa ne ga wanda yakan lalatar da abubuwa.
A man who helps not himself by his labour is brother of him that ruins himself.
10 Sunan Ubangiji hasumiya ce mai ƙarfi; masu adalci kan gudu zuwa wurinta don su zauna lafiya.
The name of the Lord is of great strength; and the righteous running to it are exalted.
11 Dukiyar masu arziki ita ce birninsu mai katanga; suna gani cewa ba za a iya huda katangar ba.
The wealth of a rich man is a strong city; and its glory casts a broad shadow.
12 Kafin fāɗuwarsa zuciyar mutum takan yi girman kai, amma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.
Before ruin a man's heart is exalted, and before honour it is humble.
13 Duk wanda yakan ba da amsa kafin ya saurara, wannan wauta ce da kuma abin kunya.
Whoso answers a word before he hears [a cause], it is folly and reproach to him.
14 Sa rai da mutum ke yi kan taimake shi sa’ad da yake ciwo, amma in ya karai, to, tasa ta ƙare.
A wise servant calms a man's anger; but who can endure a faint-hearted man?
15 Zuciya mai la’akari kan nemi sani; kunnuwan mai hikima kan bincika don yă koya.
The heart of the sensible [man] purchases discretion; and the ears of the wise seek understanding.
16 Kyauta kan buɗe hanya wa mai bayarwa yakan kuma kai shi a gaban babban mutum.
A man's gift enlarges him, and seats him among princes.
17 Wanda ya fara mai da jawabi yakan zama kamar shi ne mai gaskiya, sai wani ya fito ya yi masa tambaya tukuna.
A righteous man accuses himself at the beginning of his speech, but when he has entered upon the attack, the adversary is reproved.
18 Jefa ƙuri’a kan daidaita tsakanin masu faɗa ta kuma ajiye masu faɗan a rabe.
A silent [man] quells strifes, and determines between great powers.
19 Ɗan’uwan da aka yi wa laifi ya fi birni mai katanga wuyan shiryawa, kuma faɗace-faɗace suna kama da ƙofofin ƙarfe na fada.
A brother helped by a brother is as a strong and high city; and is [as] strong as a [well]-founded palace.
20 Daga abin da baki ya furta ne cikin mutum kan cika; girbi daga leɓunansa kuma yakan ƙoshi.
A man fills his belly with the fruits of his mouth; and he shall be satisfied with the fruits of his lips.
21 Harshe yana da ikon rai da mutuwa, kuma waɗanda suke ƙaunarsa za su ci amfaninsa.
Life and death are in the power of the tongue; and they that rule it shall eat the fruits thereof.
22 Duk wanda ya sami mace ya sami abu mai kyau ya kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
He that has found a good wife has found favours, and has received gladness from God. [He that puts away a good wife, puts away a ] [good thing, and he that keeps an adulteress is foolish and ungodly.]
23 Matalauci kan yi roƙo da taushi, amma mawadaci kan amsa da kakkausar murya.
24 Mutum mai abokai masu yawa kan lalace, amma akwai abokin da yakan manne kurkusa fiye da ɗan’uwa.

< Karin Magana 18 >