< Karin Magana 17 >

1 Gara ka ci busasshen burodi da kwanciyar rai kuma shiru da ka je cin abinci a gidan da ke cike da biki amma da ɓacin rai.
Jobb száraz darab kenyér és nyugalom mellette, mint ház tele háborúságos áldozatokkal.
2 Bawa mai hikima zai yi mulki a kan da mai rashin kunya, kuma zai raba gādo kamar ɗaya daga cikin’yan’uwansa.
Eszes szolga uralkodni fog a szégyenletes fiún, és a testvérek közt osztozkodni fog az örökségen.
3 Ana gwajin azurfa da kuma zinariya da wuta, amma Ubangiji ne mai gwajin zuciya.
Tégely az ezüstnek s kohó az aranynak, de a szívek vizsgálója az Örökkévaló.
4 Mugun mutum kan mai da hankali ga mugayen leɓuna; maƙaryaci yakan kasa kunne ga harshen ƙarairayi.
A gonosztevő figyel a jogtalanság ajkára, a hazug hallgat a veszedelem nyelvére.
5 Duk wanda yake wa matalauta ba’a yana zagin Mahaliccinsu ne; duk wanda ya yi murna akan masifar da ta sami wani za a hukunta shi.
A ki gúnyolódik a szegényen, káromolta alkotóját, a ki őrvend szerencsétlenségen, nem marad büntetlenül.
6 Jikoki rawanin tsofaffi ne, kuma iyaye su ne abin taƙamar’ya’yansu.
Az öregek koronája gyermekeik gyermekei és a gyermekek dísze a szüleik.
7 Leɓunan basira ba su dace da wawa ba, ya ma fi muni a ce mai mulki yana da leɓunan ƙarya!
Nem illő az aljashoz fennhéjázó beszéd, hát még a nemeshez hazug beszéd.
8 Cin hanci kamar sihiri yake ga wanda yake ba da shi; ko’ina ya juye, yakan yi nasara.
Bűvös kő a megvesztegetés gazdája szemeiben: bármerre fordul, boldogul.
9 Duk wanda ya rufe laifi yana inganta ƙauna ne, amma duk wanda ya yi ta maimaita batu yakan raba abokai na kusa.
A ki eltakarja a bűntettet, szeretetet keres, de a ki ismételgeti a dolgot, barátot választ el.
10 Tsawata kan sa mutum ya koyi basira fiye da abin da wawa zai koya ko da an dūke shi sau ɗari.
Mélyen hat a dorgálás az értelmesre, inkább mint mikor százszor ütik a balgát.
11 Mugayen mutane sukan kuta tawaye da Allah; za a aika manzo mutuwa a kansu.
Csak bajt keres az engedetlen, a kegyetlen követ bocsáttatik ellene.
12 Gara a haɗu da beyar da aka ƙwace wa’ya’ya fiye da a sadu da wawa cikin wautarsa.
Találjon rá az emberre kölykétől megfosztott medve, és ne a balga az ő oktalanságában.
13 In mutum ya sāka alheri da mugunta, mugunta ba za tă taɓa barin gidansa ba.
A ki rosszat fizet jóért, nem mozdul el házából a baj.
14 Farawar faɗa tana kamar ɓarkewa madatsar ruwa ne, saboda haka ka bar batun kafin faɗa ta ɓarke.
Víznek kieresztése a viszály kezdete: mielőtt kitörne, hagyd abba a pört.
15 Baratar da mai laifi a kuma hukunta mai adalci, Ubangiji ya ƙi su biyu.
A ki fölmenti a bűnöst és elítéli az igazat: az Örökkévaló utálata mindkettejük.
16 Mene ne amfanin kuɗi a hannun wawa, da yake ba shi da sha’awar samun hikima?
Minek is a vételár balgának kezében, hogy bölcsességet vegyen, s nincsen ész!
17 Aboki yakan yi ƙauna a koyaushe, ɗan’uwa kuma, ai, don ɗaukar nawayar juna ne aka haife shi.
Minden időben szeret a barát, de testvér szorongatás idejére születik.
18 Mutumin da ba shi da azanci yakan ɗauki lamunin wani ya kuma ɗauki nauyin biyan basusuwan maƙwabci.
Esztelen ember kézbe csap, kezességet vállal felebarátja előtt.
19 Duk mai son faɗa yana son zunubi, duk wanda ya gina ƙofar shiga mai tsawo yana gayyatar hallaka.
A ki a bűntettet szereti, szereti a czívódást; a ki magasra teszi bejáratát, romlást keres.
20 Mutum mai muguwar zuciya ba ya cin gaba; duk wanda yake da harshen ruɗu kan shiga wahala.
Álnok szívű nem talál jót, s a ki nyelvével ferde, bajba esik.
21 Kasance da wawa kamar ɗa yakan kawo baƙin ciki babu farin ciki ga mahaifin wawa.
A ki balgának szülője, az neki bánatára van, és nem örül az aljasnak atyja.
22 Zuciya mai farin ciki magani ne mai kyau, amma bakin rai kan busar da ƙasusuwa.
Örvendő szív jó gyógyítást ad, de a levert lélek kiszárítja a csontot.
23 Mugun mutum yakan karɓa cin hanci a asirce don yă lalace yin adalci.
Megvesztegetést vesz ki öléből a gonosz, hogy elhajlítsa a jog ösvényeit.
24 Mutum mai basira kan kafa idonsa a kan hikima, amma idanun wawa suna a kan ƙarshen duniya.
Az értelmesnek arcza előtt van a bölcsesség, de a balgának szemei föld végén járnak.
25 Da yake wawa yakan kawo baƙin ciki ga mahaifinsa da ɓacin rai ga wanda ya haife shi.
Bosszúsága atyjának a balga fiú, és keserűsége szülőanyjának.
26 Ba shi da kyau a hukunta marar laifi, ko a bulale shugaba saboda mutuncinsu.
Még bírságolni az igazat sem jó, megverni a nemeseket a méltányosság ellenére.
27 Mutum mai sani yakan yi la’akari da amfani da kalmomi, mutum mai basira kuma natsattse ne.
Visszatartja beszédét a ki tudást ismer, tartózkodó lelkű az értelmes ember,
28 Ko wawa in bai buɗe bakinsa ba, za a zaci shi mai hikima ne, da kuma mai basira inda ya ƙame bakinsa.
Az oktalan is, midőn hallgat, bölcsnek tekintetik, a ki becsukja ajkait, értelmesnek.

< Karin Magana 17 >