< Karin Magana 16 >
1 Ga mutum ne shirye-shiryen zuciya suke, amma daga Ubangiji ne amshin harshe kan zo.
Do homem são os planejamentos do coração, mas a reposta da boca [vem] do SENHOR.
2 Dukan hanyoyin mutum sukan yi kamar marar laifi ne gare shi, amma Ubangiji yakan auna manufofi.
Todos os caminhos do homem são puros aos seus [próprios] olhos; mas o SENHOR pesa os espíritos.
3 Ka miƙa wa Ubangiji dukan abin da kake yi, shirye-shiryenka kuwa za su yi nasara.
Confia tuas obras ao SENHOR, e teus pensamentos serão firmados.
4 Ubangiji yana yin kome domin amfaninsa, har ma da mugaye domin ranar masifa.
O SENHOR fez tudo para seu propósito; e até ao perverso para o dia do mal.
5 Ubangiji yana ƙyamar dukan zuciya mai girman kai. Ka tabbata da wannan. Ba za su kuɓuta daga hukunci ba.
O SENHOR abomina todo orgulhoso de coração; certamente não ficará impune.
6 Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.
Com misericórdia e fidelidade a perversidade é reconciliada; e com o temor ao SENHOR se desvia do mal.
7 Sa’ad da hanyoyin mutum sun gamshi Ubangiji, yakan sa abokan gāban mutumin ma su zauna lafiya da shi.
Quando os caminhos do homem são agradáveis ao SENHOR, ele faz até seus inimigos terem paz com ele.
8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar adalci da sami riba mai yawa ta hanyar rashin gaskiya.
Melhor é o pouco com justiça, do que a abundância de rendas com injustiça.
9 ’Yan Adam sukan yi shirye-shiryensu a zukatansu, amma Ubangiji ne yake da ikon cika matakansa.
O coração do homem planeja seu caminho, mas é o SENHOR que dirige seus passos.
10 Leɓunan sarki kan yi magana kamar ta wurin ikon Allah, kuma bai kamata bakinsa ya yi kuskure a yanke shari’a ba.
Nos lábios do rei estão palavras sublimes; sua boca não transgride quando julga.
11 Ma’aunai da magwajin gaskiya daga Ubangiji ne; dukan ma’aunai da suke cikin jaka yinsa ne.
O peso e a balança justos pertencem ao SENHOR; a ele pertencem todos os pesos da bolsa.
12 Sarakuna suna ƙyamar abin da ba shi da kyau, gama an kafa kujerar sarauta ta wurin adalci ne.
Os reis abominam fazer perversidade, porque com justiça é que se confirma o trono.
13 Sarakuna sukan ji daɗi leɓuna masu yin gaskiya; sukan darjanta mutumin da yake faɗin gaskiya.
Os lábios justos são do agrado dos reis, e eles amam ao que fala palavras direitas.
14 Fushin sarki ɗan saƙon mutuwa ne, amma mai hikima yakan faranta masa rai.
A ira do rei é como mensageiros de morte; mas o homem sábio a apaziguará.
15 Sa’ad da fuskar sarki ta haska, yana nufin rai ke nan; tagomashinsa yana kamar girgijen ruwa a bazara.
No brilho do rosto do rei há vida; e seu favor é como uma nuvem de chuva tardia.
16 Ya ma fi kyau ka sami hikima fiye da zinariya, ka zaɓi fahimi a maimakon azurfa!
Obter sabedoria é tão melhor do que o ouro! E obter sabedoria é mais excelente do que a prata.
17 Buɗaɗɗiyar hanyar masu aikata gaskiya kan guje wa mugunta; duk wanda yake lura da hanyarsa yakan lura da ransa.
A estrada dos corretos se afasta do mal; e guarda sua alma quem vigia seu caminho.
18 Girmankai yakan zo kafin hallaka, girman kai yakan zo kafin fāɗuwa.
Antes da destruição vem a arrogância, e antes da queda vem a soberba de espírito.
19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu sauƙinkai, da ka raba ganima da masu girman kai.
É melhor ser humilde de espírito com os mansos, do que repartir despojos com os arrogantes.
20 Duk wanda ya mai da hankali ga umarni yakan yi nasara, kuma mai albarka ne wanda yake dogara ga Ubangiji.
Aquele que pensa prudentemente na palavra encontrará o bem; e quem confia no SENHOR é bem-aventurado.
21 Akan ce da masu hikima a zuciya hazikai, kuma kalmomi masu daɗi kan inganta umarni.
O sábio de coração será chamado de prudente; e a doçura dos lábios aumentará a instrução.
22 Fahimi shi ne maɓulɓular rai ga waɗanda suke da shi, amma wauta kan kawo hukunci ga wawaye.
Manancial de vida é o entendimento, para queles que o possuem; mas a instrução dos tolos é loucura.
23 Zuciyar mai hikima kan bi da bakinsa, kuma leɓunansa kan inganta umarni.
O coração do sábio dá prudência à sua boca; e sobre seus lábios aumentará a instrução.
24 Kalmomi masu daɗi suna kama da kakin zuma, mai zaƙi ga rai da kuma warkarwa ga ƙasusuwa.
Favo de mel são as palavras suaves: doces para a alma, e remédio para os ossos.
25 Akwai hanyar da ta yi kamar daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
Há um caminho que parece direito ao homem, porém seu fim são caminhos de morte.
26 Marmarin cin abinci yakan yi wa ɗan ƙodago aiki; yunwarsa kan sa ya ci gaba.
A alma do trabalhador faz ele trabalhar para si, porque sua boca o obriga.
27 Mutumin banza yakan ƙulla mugunta, kuma jawabinsa yana kama da wuta mai ƙuna.
O homem maligno cava o mal, e em seus lábios [há] como que um fogo ardente.
28 Fitinannen mutum yakan zuga tashin hankali, mai gulma kuma yakan raba abokai na kusa.
O homem perverso levanta contenda, e o difamador faz [até] grandes amigos se separarem.
29 Mutum mai tā-da-na-zaune-tsaye yakan ruɗi maƙwabcinsa ya kai shi a hanyar da ba ta da kyau.
O homem violento ilude a seu próximo, e o guia por um caminho que não é bom.
30 Duk wanda ya ƙyifce da idonsa yana ƙulla maƙarƙashiya ce; duk wanda ya murguɗa leɓunansa yana niyya aikata mugunta ke nan.
Ele fecha seus olhos para imaginar perversidades; ele aperta os lábios para praticar o mal.
31 Furfura rawani ne mai daraja; akan same ta ta wurin yin rayuwa ta adalci.
Cabelos grisalhos são uma coroa de honra, [caso] se encontrem no caminho de justiça.
32 Gara ka zama mai haƙuri da ka zama jarumi, ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
Melhor é o que demora para se irritar do que o valente; e [melhor é] aquele que domina seu espírito do que aquele que toma uma cidade.
33 Akan jefa ƙuri’a a kan cinya, amma kowace shawara mai kyau daga Ubangiji ne.
A sorte é lançada no colo, mas toda decisão pertence ao SENHOR.