< Karin Magana 16 >

1 Ga mutum ne shirye-shiryen zuciya suke, amma daga Ubangiji ne amshin harshe kan zo.
Umuntu angawabumba amacebo ngenhliziyo yakhe, kodwa uThixo nguye omupha amazwi okuwachaza.
2 Dukan hanyoyin mutum sukan yi kamar marar laifi ne gare shi, amma Ubangiji yakan auna manufofi.
Umuntu angabona sengathi zonke izindlela zakhe ziqondile, kodwa uThixo uyazihlolisisa zonke injongo zomuntu.
3 Ka miƙa wa Ubangiji dukan abin da kake yi, shirye-shiryenka kuwa za su yi nasara.
Nikela kuThixo konke okwenzayo, kuzaphumelelisa wonke amacebo akho.
4 Ubangiji yana yin kome domin amfaninsa, har ma da mugaye domin ranar masifa.
UThixo uzilungisele isiphetho sakho konke kanye lababi usuku lokubhujiswa.
5 Ubangiji yana ƙyamar dukan zuciya mai girman kai. Ka tabbata da wannan. Ba za su kuɓuta daga hukunci ba.
UThixo uyabazonda bonke abazikhukhumezayo. Ngempela kabayikuphepha ukujeziswa.
6 Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.
Isono siyahlawulelwa ngothando langokwethembeka; ngokwesaba uThixo umuntu uyaphepha ebubini.
7 Sa’ad da hanyoyin mutum sun gamshi Ubangiji, yakan sa abokan gāban mutumin ma su zauna lafiya da shi.
Nxa izindlela zomuntu zimthokozisa uThixo, uyenza lezitha zakhe zihlalisane laye ngokuthula.
8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar adalci da sami riba mai yawa ta hanyar rashin gaskiya.
Kungcono ukuzuza okulutshwana ngendlela elungileyo kulokuzuza okunengi ngobuqili.
9 ’Yan Adam sukan yi shirye-shiryensu a zukatansu, amma Ubangiji ne yake da ikon cika matakansa.
Umuntu angalungisa indlela yakhe engqondweni yakhe, kodwa uThixo nguye olawula izinyathelo zakhe.
10 Leɓunan sarki kan yi magana kamar ta wurin ikon Allah, kuma bai kamata bakinsa ya yi kuskure a yanke shari’a ba.
Izindebe zombusi zikhuluma kungathi lidlozi ngakho umlomo wakhe kawungaphambuli umthetho.
11 Ma’aunai da magwajin gaskiya daga Ubangiji ne; dukan ma’aunai da suke cikin jaka yinsa ne.
Izilinganiso eziqondileyo zivela kuThixo; zonke izisindo ezisemgodleni zenziwa nguye.
12 Sarakuna suna ƙyamar abin da ba shi da kyau, gama an kafa kujerar sarauta ta wurin adalci ne.
Amakhosi ayakuzonda ukwenza okubi, ngoba isihlalo sobukhosi sakhelwe phezu kokulunga.
13 Sarakuna sukan ji daɗi leɓuna masu yin gaskiya; sukan darjanta mutumin da yake faɗin gaskiya.
Amakhosi athokoziswa yizindebe ezithembekileyo; ayamazisa umuntu okhuluma iqiniso.
14 Fushin sarki ɗan saƙon mutuwa ne, amma mai hikima yakan faranta masa rai.
Ulaka lwenkosi luyisithunywa sokufa, kodwa umuntu ohlakaniphileyo uyaluxolisa.
15 Sa’ad da fuskar sarki ta haska, yana nufin rai ke nan; tagomashinsa yana kamar girgijen ruwa a bazara.
Nxa ubuso benkosi bulentokozo, kukhomba ukuphila; ukuthandwa yiyo kunjengeyezi lezulu entwasa.
16 Ya ma fi kyau ka sami hikima fiye da zinariya, ka zaɓi fahimi a maimakon azurfa!
Kungcono kangakanani ukuzuza ukuhlakanipha kulegolide, ukukhetha ukuzwisisa kulesiliva!
17 Buɗaɗɗiyar hanyar masu aikata gaskiya kan guje wa mugunta; duk wanda yake lura da hanyarsa yakan lura da ransa.
Umgwaqo womuntu oqotho uceza ububi; lowo onanzelelayo indlela yakhe unanzelela impilo yakhe.
18 Girmankai yakan zo kafin hallaka, girman kai yakan zo kafin fāɗuwa.
Ukuzigqaja kwandulela ukubhujiswa, umoya omubi ulandelwa yikuwa.
19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu sauƙinkai, da ka raba ganima da masu girman kai.
Kungcono umoya othobekileyo lokuhlala kwabancindezelweyo kulokwabelana impango labazigqajayo.
20 Duk wanda ya mai da hankali ga umarni yakan yi nasara, kuma mai albarka ne wanda yake dogara ga Ubangiji.
Lowo olalela izeluleko uyaphumelela, njalo ubusisiwe lowo othemba uThixo.
21 Akan ce da masu hikima a zuciya hazikai, kuma kalmomi masu daɗi kan inganta umarni.
Abahlakaniphileyo enhliziyweni kuthiwa bayaqedisisa, njalo amazwi amnandi aqinisa izeluleko.
22 Fahimi shi ne maɓulɓular rai ga waɗanda suke da shi, amma wauta kan kawo hukunci ga wawaye.
Ukuzwisisa kungumthombo wokuphila kulabo abalakho, kodwa ubuwula buletha isijeziso eziwuleni.
23 Zuciyar mai hikima kan bi da bakinsa, kuma leɓunansa kan inganta umarni.
Inhliziyo yomuntu ohlakaniphileyo ikhokhela umlomo wakhe, kanti lezindebe zakhe zikhuthaza izeluleko.
24 Kalmomi masu daɗi suna kama da kakin zuma, mai zaƙi ga rai da kuma warkarwa ga ƙasusuwa.
Amazwi amahle alikhekheba loluju, amnandi emphefumulweni njalo ayelapha emathanjeni.
25 Akwai hanyar da ta yi kamar daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
Kukhona indlela ebonakala ilungile emuntwini, kodwa isiphetho sayo siyikufa.
26 Marmarin cin abinci yakan yi wa ɗan ƙodago aiki; yunwarsa kan sa ya ci gaba.
Isisebenzi sifuqwa liphango ukusebenza kakhulu; ukulamba yikho okusikhuthazayo.
27 Mutumin banza yakan ƙulla mugunta, kuma jawabinsa yana kama da wuta mai ƙuna.
Isixhwali siceba ububi, lenkulumo yaso injengomlilo ohaqazayo.
28 Fitinannen mutum yakan zuga tashin hankali, mai gulma kuma yakan raba abokai na kusa.
Umuntu ongelangqondo udaza inkani, njalo lomuntu onyeyayo wehlukanisa abangane.
29 Mutum mai tā-da-na-zaune-tsaye yakan ruɗi maƙwabcinsa ya kai shi a hanyar da ba ta da kyau.
Umuntu wodlakela uhuga umakhelwane wakhe amholele endleleni engalunganga.
30 Duk wanda ya ƙyifce da idonsa yana ƙulla maƙarƙashiya ce; duk wanda ya murguɗa leɓunansa yana niyya aikata mugunta ke nan.
Lowo ofica ngelihlo lakhe uceba izibozi; lowo oluma indebe zakhe uqonde ububi.
31 Furfura rawani ne mai daraja; akan same ta ta wurin yin rayuwa ta adalci.
Inwele ezimhlophe zingumqhele wobukhulu, zizuzwa ngempilo elungileyo.
32 Gara ka zama mai haƙuri da ka zama jarumi, ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
Ungcono umuntu obekezelayo kuleqhawe, umuntu ozinqandayo ulaka lwakhe kulalowo othumba idolobho.
33 Akan jefa ƙuri’a a kan cinya, amma kowace shawara mai kyau daga Ubangiji ne.
Inkatho iphoselwa enkundleni, kodwa isinqumo sayo sisemandleni kaThixo.

< Karin Magana 16 >