< Karin Magana 16 >

1 Ga mutum ne shirye-shiryen zuciya suke, amma daga Ubangiji ne amshin harshe kan zo.
Les projets du cœur dépendent de l'homme; mais la réponse de la langue appartient à l'Éternel.
2 Dukan hanyoyin mutum sukan yi kamar marar laifi ne gare shi, amma Ubangiji yakan auna manufofi.
Toutes les voies de l'homme lui semblent pures; c'est l'Éternel qui pèse les esprits.
3 Ka miƙa wa Ubangiji dukan abin da kake yi, shirye-shiryenka kuwa za su yi nasara.
Remets tes affaires à l'Éternel, et tes desseins seront affermis.
4 Ubangiji yana yin kome domin amfaninsa, har ma da mugaye domin ranar masifa.
L'Éternel a fait toutes choses en sorte qu'elles répondent l'une à l'autre, et même le méchant pour le jour de la calamité.
5 Ubangiji yana ƙyamar dukan zuciya mai girman kai. Ka tabbata da wannan. Ba za su kuɓuta daga hukunci ba.
L'Éternel a en abomination tout homme hautain de cœur; tôt ou tard il ne demeurera point impuni.
6 Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.
L'iniquité sera expiée par la miséricorde et la vérité; et par la crainte de l'Éternel on se détourne du mal.
7 Sa’ad da hanyoyin mutum sun gamshi Ubangiji, yakan sa abokan gāban mutumin ma su zauna lafiya da shi.
Quand l'Éternel prend plaisir aux voies d'un homme, il apaise envers lui même ses ennemis.
8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar adalci da sami riba mai yawa ta hanyar rashin gaskiya.
Peu, avec justice, vaut mieux que de grands revenus sans droit.
9 ’Yan Adam sukan yi shirye-shiryensu a zukatansu, amma Ubangiji ne yake da ikon cika matakansa.
Le cœur de l'homme délibère sur sa conduite; mais l'Éternel dirige ses pas.
10 Leɓunan sarki kan yi magana kamar ta wurin ikon Allah, kuma bai kamata bakinsa ya yi kuskure a yanke shari’a ba.
Des oracles sont sur les lèvres du roi, et sa bouche ne s'écarte point du droit.
11 Ma’aunai da magwajin gaskiya daga Ubangiji ne; dukan ma’aunai da suke cikin jaka yinsa ne.
La balance et le poids juste viennent de l'Éternel, et tous les poids du sachet sont son œuvre.
12 Sarakuna suna ƙyamar abin da ba shi da kyau, gama an kafa kujerar sarauta ta wurin adalci ne.
Les rois doivent avoir horreur de faire le mal, car c'est la justice qui affermit le trône.
13 Sarakuna sukan ji daɗi leɓuna masu yin gaskiya; sukan darjanta mutumin da yake faɗin gaskiya.
Les rois doivent prendre plaisir aux paroles justes, et aimer celui qui parle avec droiture.
14 Fushin sarki ɗan saƙon mutuwa ne, amma mai hikima yakan faranta masa rai.
La fureur du roi est un messager de mort; mais l'homme sage l'apaise.
15 Sa’ad da fuskar sarki ta haska, yana nufin rai ke nan; tagomashinsa yana kamar girgijen ruwa a bazara.
Le visage serein du roi donne la vie; et sa faveur est comme la nuée qui porte la pluie de l'arrière-saison.
16 Ya ma fi kyau ka sami hikima fiye da zinariya, ka zaɓi fahimi a maimakon azurfa!
Combien il vaut mieux acquérir de la sagesse que de l'or fin! Et combien il est plus excellent d'acquérir de la prudence que de l'argent!
17 Buɗaɗɗiyar hanyar masu aikata gaskiya kan guje wa mugunta; duk wanda yake lura da hanyarsa yakan lura da ransa.
Le chemin des hommes droits, c'est de se détourner du mal; celui-là garde son âme qui prend garde à sa conduite.
18 Girmankai yakan zo kafin hallaka, girman kai yakan zo kafin fāɗuwa.
L'orgueil va devant l'écrasement, et la fierté d'esprit devant la ruine.
19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu sauƙinkai, da ka raba ganima da masu girman kai.
Il vaut mieux être humble avec les débonnaires, que de partager le butin avec les orgueilleux.
20 Duk wanda ya mai da hankali ga umarni yakan yi nasara, kuma mai albarka ne wanda yake dogara ga Ubangiji.
Celui qui prend garde à la parole, trouvera le bien; et celui qui se confie en l'Éternel, sera heureux.
21 Akan ce da masu hikima a zuciya hazikai, kuma kalmomi masu daɗi kan inganta umarni.
On appellera intelligent celui qui a un cœur sage; et la douceur des paroles augmente la science.
22 Fahimi shi ne maɓulɓular rai ga waɗanda suke da shi, amma wauta kan kawo hukunci ga wawaye.
La prudence est à ceux qui la possèdent une source de vie; mais le châtiment des insensés, c'est leur folie.
23 Zuciyar mai hikima kan bi da bakinsa, kuma leɓunansa kan inganta umarni.
Le cœur sage conduit prudemment sa bouche, et ajoute la science à ses lèvres.
24 Kalmomi masu daɗi suna kama da kakin zuma, mai zaƙi ga rai da kuma warkarwa ga ƙasusuwa.
Les paroles agréables sont des rayons de miel, une douceur à l'âme, et la santé aux os.
25 Akwai hanyar da ta yi kamar daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
Il y a telle voie qui semble droite à l'homme, mais dont l'issue est la voie de la mort.
26 Marmarin cin abinci yakan yi wa ɗan ƙodago aiki; yunwarsa kan sa ya ci gaba.
La faim de celui qui travaille, travaille pour lui, parce que sa bouche l'y contraint.
27 Mutumin banza yakan ƙulla mugunta, kuma jawabinsa yana kama da wuta mai ƙuna.
L'homme méchant se creuse le mal, et il y a comme un feu brûlant sur ses lèvres.
28 Fitinannen mutum yakan zuga tashin hankali, mai gulma kuma yakan raba abokai na kusa.
L'homme pervers sème des querelles, et le rapporteur divise les meilleurs amis.
29 Mutum mai tā-da-na-zaune-tsaye yakan ruɗi maƙwabcinsa ya kai shi a hanyar da ba ta da kyau.
L'homme violent entraîne son compagnon, et le fait marcher dans une voie qui n'est pas bonne.
30 Duk wanda ya ƙyifce da idonsa yana ƙulla maƙarƙashiya ce; duk wanda ya murguɗa leɓunansa yana niyya aikata mugunta ke nan.
Celui qui ferme les yeux pour méditer le mal, celui qui serre les lèvres, a déjà accompli le crime.
31 Furfura rawani ne mai daraja; akan same ta ta wurin yin rayuwa ta adalci.
Les cheveux blancs sont une couronne d'honneur; c'est dans la voie de la justice qu'elle se trouve.
32 Gara ka zama mai haƙuri da ka zama jarumi, ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
Celui qui est lent à la colère vaut mieux que l'homme vaillant; et celui qui est maître de son cœur, que celui qui prend des villes.
33 Akan jefa ƙuri’a a kan cinya, amma kowace shawara mai kyau daga Ubangiji ne.
On jette le sort dans le pan de la robe; mais tout ce qui en résulte vient de l'Éternel.

< Karin Magana 16 >