< Karin Magana 16 >

1 Ga mutum ne shirye-shiryen zuciya suke, amma daga Ubangiji ne amshin harshe kan zo.
Les projets que forme le cœur dépendent de l’homme, Mais la réponse que donne la bouche vient de l’Éternel.
2 Dukan hanyoyin mutum sukan yi kamar marar laifi ne gare shi, amma Ubangiji yakan auna manufofi.
Toutes les voies de l’homme sont pures à ses yeux; Mais celui qui pèse les esprits, c’est l’Éternel.
3 Ka miƙa wa Ubangiji dukan abin da kake yi, shirye-shiryenka kuwa za su yi nasara.
Recommande à l’Éternel tes œuvres, Et tes projets réussiront.
4 Ubangiji yana yin kome domin amfaninsa, har ma da mugaye domin ranar masifa.
L’Éternel a tout fait pour un but, Même le méchant pour le jour du malheur.
5 Ubangiji yana ƙyamar dukan zuciya mai girman kai. Ka tabbata da wannan. Ba za su kuɓuta daga hukunci ba.
Tout cœur hautain est en abomination à l’Éternel; Certes, il ne restera pas impuni.
6 Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.
Par la bonté et la fidélité on expie l’iniquité, Et par la crainte de l’Éternel on se détourne du mal.
7 Sa’ad da hanyoyin mutum sun gamshi Ubangiji, yakan sa abokan gāban mutumin ma su zauna lafiya da shi.
Quand l’Éternel approuve les voies d’un homme, Il dispose favorablement à son égard même ses ennemis.
8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar adalci da sami riba mai yawa ta hanyar rashin gaskiya.
Mieux vaut peu, avec la justice, Que de grands revenus, avec l’injustice.
9 ’Yan Adam sukan yi shirye-shiryensu a zukatansu, amma Ubangiji ne yake da ikon cika matakansa.
Le cœur de l’homme médite sa voie, Mais c’est l’Éternel qui dirige ses pas.
10 Leɓunan sarki kan yi magana kamar ta wurin ikon Allah, kuma bai kamata bakinsa ya yi kuskure a yanke shari’a ba.
Des oracles sont sur les lèvres du roi: Sa bouche ne doit pas être infidèle quand il juge.
11 Ma’aunai da magwajin gaskiya daga Ubangiji ne; dukan ma’aunai da suke cikin jaka yinsa ne.
Le poids et la balance justes sont à l’Éternel; Tous les poids du sac sont son ouvrage.
12 Sarakuna suna ƙyamar abin da ba shi da kyau, gama an kafa kujerar sarauta ta wurin adalci ne.
Les rois ont horreur de faire le mal, Car c’est par la justice que le trône s’affermit.
13 Sarakuna sukan ji daɗi leɓuna masu yin gaskiya; sukan darjanta mutumin da yake faɗin gaskiya.
Les lèvres justes gagnent la faveur des rois, Et ils aiment celui qui parle avec droiture.
14 Fushin sarki ɗan saƙon mutuwa ne, amma mai hikima yakan faranta masa rai.
La fureur du roi est un messager de mort, Et un homme sage doit l’apaiser.
15 Sa’ad da fuskar sarki ta haska, yana nufin rai ke nan; tagomashinsa yana kamar girgijen ruwa a bazara.
La sérénité du visage du roi donne la vie, Et sa faveur est comme une pluie du printemps.
16 Ya ma fi kyau ka sami hikima fiye da zinariya, ka zaɓi fahimi a maimakon azurfa!
Combien acquérir la sagesse vaut mieux que l’or! Combien acquérir l’intelligence est préférable à l’argent!
17 Buɗaɗɗiyar hanyar masu aikata gaskiya kan guje wa mugunta; duk wanda yake lura da hanyarsa yakan lura da ransa.
Le chemin des hommes droits, c’est d’éviter le mal; Celui qui garde son âme veille sur sa voie.
18 Girmankai yakan zo kafin hallaka, girman kai yakan zo kafin fāɗuwa.
L’arrogance précède la ruine, Et l’orgueil précède la chute.
19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu sauƙinkai, da ka raba ganima da masu girman kai.
Mieux vaut être humble avec les humbles Que de partager le butin avec les orgueilleux.
20 Duk wanda ya mai da hankali ga umarni yakan yi nasara, kuma mai albarka ne wanda yake dogara ga Ubangiji.
Celui qui réfléchit sur les choses trouve le bonheur, Et celui qui se confie en l’Éternel est heureux.
21 Akan ce da masu hikima a zuciya hazikai, kuma kalmomi masu daɗi kan inganta umarni.
Celui qui est sage de cœur est appelé intelligent, Et la douceur des lèvres augmente le savoir.
22 Fahimi shi ne maɓulɓular rai ga waɗanda suke da shi, amma wauta kan kawo hukunci ga wawaye.
La sagesse est une source de vie pour celui qui la possède; Et le châtiment des insensés, c’est leur folie.
23 Zuciyar mai hikima kan bi da bakinsa, kuma leɓunansa kan inganta umarni.
Celui qui est sage de cœur manifeste la sagesse par sa bouche, Et l’accroissement de son savoir paraît sur ses lèvres.
24 Kalmomi masu daɗi suna kama da kakin zuma, mai zaƙi ga rai da kuma warkarwa ga ƙasusuwa.
Les paroles agréables sont un rayon de miel, Douces pour l’âme et salutaires pour le corps.
25 Akwai hanyar da ta yi kamar daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
Telle voie paraît droite à un homme, Mais son issue, c’est la voie de la mort.
26 Marmarin cin abinci yakan yi wa ɗan ƙodago aiki; yunwarsa kan sa ya ci gaba.
Celui qui travaille, travaille pour lui, Car sa bouche l’y excite.
27 Mutumin banza yakan ƙulla mugunta, kuma jawabinsa yana kama da wuta mai ƙuna.
L’homme pervers prépare le malheur, Et il y a sur ses lèvres comme un feu ardent.
28 Fitinannen mutum yakan zuga tashin hankali, mai gulma kuma yakan raba abokai na kusa.
L’homme pervers excite des querelles, Et le rapporteur divise les amis.
29 Mutum mai tā-da-na-zaune-tsaye yakan ruɗi maƙwabcinsa ya kai shi a hanyar da ba ta da kyau.
L’homme violent séduit son prochain, Et le fait marcher dans une voie qui n’est pas bonne.
30 Duk wanda ya ƙyifce da idonsa yana ƙulla maƙarƙashiya ce; duk wanda ya murguɗa leɓunansa yana niyya aikata mugunta ke nan.
Celui qui ferme les yeux pour se livrer à des pensées perverses, Celui qui se mord les lèvres, a déjà consommé le mal.
31 Furfura rawani ne mai daraja; akan same ta ta wurin yin rayuwa ta adalci.
Les cheveux blancs sont une couronne d’honneur; C’est dans le chemin de la justice qu’on la trouve.
32 Gara ka zama mai haƙuri da ka zama jarumi, ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
Celui qui est lent à la colère vaut mieux qu’un héros, Et celui qui est maître de lui-même, que celui qui prend des villes.
33 Akan jefa ƙuri’a a kan cinya, amma kowace shawara mai kyau daga Ubangiji ne.
On jette le sort dans le pan de la robe, Mais toute décision vient de l’Éternel.

< Karin Magana 16 >