< Karin Magana 16 >

1 Ga mutum ne shirye-shiryen zuciya suke, amma daga Ubangiji ne amshin harshe kan zo.
L’Homme est maître des résolutions de son cœur; mais c’est l’Eternel qui prononce sur elles.
2 Dukan hanyoyin mutum sukan yi kamar marar laifi ne gare shi, amma Ubangiji yakan auna manufofi.
Toutes les voies de l’homme sont pures à ses yeux, mais l’Eternel sonde les esprits.
3 Ka miƙa wa Ubangiji dukan abin da kake yi, shirye-shiryenka kuwa za su yi nasara.
Remets le succès de tes œuvres à l’Eternel, et tes projets s’en trouveront affermis.
4 Ubangiji yana yin kome domin amfaninsa, har ma da mugaye domin ranar masifa.
L’Eternel a tout fait pour un but prédestiné, même le méchant pour le jour du malheur.
5 Ubangiji yana ƙyamar dukan zuciya mai girman kai. Ka tabbata da wannan. Ba za su kuɓuta daga hukunci ba.
Tout cœur hautain est en horreur à l’Eternel: haut la main! il ne restera pas indemne.
6 Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.
La bonté et la bienveillance effacent la faute; la crainte de l’Eternel fait éviter le mal.
7 Sa’ad da hanyoyin mutum sun gamshi Ubangiji, yakan sa abokan gāban mutumin ma su zauna lafiya da shi.
Dieu agrée-t-il les voies d’un homme, il lui concilie même la faveur de ses ennemis.
8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar adalci da sami riba mai yawa ta hanyar rashin gaskiya.
Mieux vaut une honnête médiocrité qu’un grand revenu, acquis par l’improbité.
9 ’Yan Adam sukan yi shirye-shiryensu a zukatansu, amma Ubangiji ne yake da ikon cika matakansa.
Le cœur de l’homme choisit sa voie; mais l’Eternel dirige ses pas.
10 Leɓunan sarki kan yi magana kamar ta wurin ikon Allah, kuma bai kamata bakinsa ya yi kuskure a yanke shari’a ba.
Ce sont des oracles qui émanent des lèvres du roi: quand il rend la justice, sa bouche ne faillit pas.
11 Ma’aunai da magwajin gaskiya daga Ubangiji ne; dukan ma’aunai da suke cikin jaka yinsa ne.
Les plateaux, les balances exactes sont choses de Dieu, il est l’auteur de tous les justes poids.
12 Sarakuna suna ƙyamar abin da ba shi da kyau, gama an kafa kujerar sarauta ta wurin adalci ne.
Faire le mal est chose odieuse aux rois; car les trônes s’affermissent par la justice.
13 Sarakuna sukan ji daɗi leɓuna masu yin gaskiya; sukan darjanta mutumin da yake faɗin gaskiya.
Des lèvres loyales font plaisir aux rois; ils aiment qui parle avec droiture.
14 Fushin sarki ɗan saƙon mutuwa ne, amma mai hikima yakan faranta masa rai.
Le courroux du roi est un messager de mort, un homme sage sait l’apaiser.
15 Sa’ad da fuskar sarki ta haska, yana nufin rai ke nan; tagomashinsa yana kamar girgijen ruwa a bazara.
Que le visage du roi s’éclaire, c’est un gage de vie; sa faveur est comme une nuée chargée de pluie printanière.
16 Ya ma fi kyau ka sami hikima fiye da zinariya, ka zaɓi fahimi a maimakon azurfa!
Acquérir la sagesse, combien cela est plus précieux que l’or fin! S’Enrichir en sagacité vaut mieux que l’argent.
17 Buɗaɗɗiyar hanyar masu aikata gaskiya kan guje wa mugunta; duk wanda yake lura da hanyarsa yakan lura da ransa.
La route des justes les éloigne du mal; qui suit droit son chemin préserve sa vie.
18 Girmankai yakan zo kafin hallaka, girman kai yakan zo kafin fāɗuwa.
L’Orgueil précède la ruine, l’arrogance est le signe avant-coureur de la chute.
19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu sauƙinkai, da ka raba ganima da masu girman kai.
Prendre une attitude modeste avec les humbles vaut mieux que partager du butin avec les orgueilleux.
20 Duk wanda ya mai da hankali ga umarni yakan yi nasara, kuma mai albarka ne wanda yake dogara ga Ubangiji.
Qui réfléchit mûrement à une affaire s’assure des avantages; mais heureux qui met sa confiance en l’Eternel!
21 Akan ce da masu hikima a zuciya hazikai, kuma kalmomi masu daɗi kan inganta umarni.
Qui a le cœur sage mérite d’être appelé intelligent; la douceur des lèvres augmente la force de persuasion.
22 Fahimi shi ne maɓulɓular rai ga waɗanda suke da shi, amma wauta kan kawo hukunci ga wawaye.
L’Intelligence est une source de vie pour celui qui en est doué; le châtiment des sots, c’est leur sottise.
23 Zuciyar mai hikima kan bi da bakinsa, kuma leɓunansa kan inganta umarni.
Le cœur du sage inspire sa bouche, et augmente la force de persuasion de ses lèvres.
24 Kalmomi masu daɗi suna kama da kakin zuma, mai zaƙi ga rai da kuma warkarwa ga ƙasusuwa.
Des paroles amènes sont un rayon de miel, doux à l’âme, bienfaisant au corps.
25 Akwai hanyar da ta yi kamar daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
Tel chemin paraît tout uni à l’homme, et il aboutit aux avenues de la mort.
26 Marmarin cin abinci yakan yi wa ɗan ƙodago aiki; yunwarsa kan sa ya ci gaba.
C’Est pour lui-même que travaille le laborieux, car pressantes sont les exigences de sa bouche.
27 Mutumin banza yakan ƙulla mugunta, kuma jawabinsa yana kama da wuta mai ƙuna.
L’Homme sans valeur morale est un artisan de malheur; sur ses lèvres il y a comme un feu dévorant.
28 Fitinannen mutum yakan zuga tashin hankali, mai gulma kuma yakan raba abokai na kusa.
L’Homme artificieux déchaîne la discorde; le boutefeu sème la division entre amis.
29 Mutum mai tā-da-na-zaune-tsaye yakan ruɗi maƙwabcinsa ya kai shi a hanyar da ba ta da kyau.
L’Homme violent circonvient son prochain et le mène dans une mauvaise voie.
30 Duk wanda ya ƙyifce da idonsa yana ƙulla maƙarƙashiya ce; duk wanda ya murguɗa leɓunansa yana niyya aikata mugunta ke nan.
Il ferme les yeux pour méditer de mauvais coups; il se pince les lèvres: il a consommé le mal!
31 Furfura rawani ne mai daraja; akan same ta ta wurin yin rayuwa ta adalci.
La haute vieillesse est une couronne d’honneur; c’est sur le chemin de la vertu qu’elle se rencontre.
32 Gara ka zama mai haƙuri da ka zama jarumi, ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
Qui résiste à la colère l’emporte sur le héros; qui domine ses passionssur un preneur de villes.
33 Akan jefa ƙuri’a a kan cinya, amma kowace shawara mai kyau daga Ubangiji ne.
On agite le sort dans l’urne mais l’arrêt qu’il prononce vient de l’Eternel.

< Karin Magana 16 >