< Karin Magana 16 >
1 Ga mutum ne shirye-shiryen zuciya suke, amma daga Ubangiji ne amshin harshe kan zo.
To man belongeth the preparation of the heart; But the answer of the tongue is from the LORD.
2 Dukan hanyoyin mutum sukan yi kamar marar laifi ne gare shi, amma Ubangiji yakan auna manufofi.
All the ways of a man are pure in his own eyes; But the LORD weigheth the spirit.
3 Ka miƙa wa Ubangiji dukan abin da kake yi, shirye-shiryenka kuwa za su yi nasara.
Commit thy doings to the LORD, And thy purposes shall be established.
4 Ubangiji yana yin kome domin amfaninsa, har ma da mugaye domin ranar masifa.
The LORD hath ordained every thing for its end; Yea, even the wicked for the day of evil.
5 Ubangiji yana ƙyamar dukan zuciya mai girman kai. Ka tabbata da wannan. Ba za su kuɓuta daga hukunci ba.
Every one that is proud in heart is an abomination to the LORD; From generation to generation he shall not be unpunished.
6 Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.
Through kindness and truth, iniquity is expiated; And, through the fear of the LORD, men depart from evil.
7 Sa’ad da hanyoyin mutum sun gamshi Ubangiji, yakan sa abokan gāban mutumin ma su zauna lafiya da shi.
When a man's ways please the LORD, He maketh even his enemies to be at peace with him.
8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar adalci da sami riba mai yawa ta hanyar rashin gaskiya.
Better is a little with righteousness, Than great revenues without right.
9 ’Yan Adam sukan yi shirye-shiryensu a zukatansu, amma Ubangiji ne yake da ikon cika matakansa.
The heart of man deviseth his way, But the LORD establisheth his steps.
10 Leɓunan sarki kan yi magana kamar ta wurin ikon Allah, kuma bai kamata bakinsa ya yi kuskure a yanke shari’a ba.
A divine sentence is upon the lips of a king; His mouth transgresseth not in judgment.
11 Ma’aunai da magwajin gaskiya daga Ubangiji ne; dukan ma’aunai da suke cikin jaka yinsa ne.
A just balance and scales are the appointment of the LORD; All the weights of the bag are his work.
12 Sarakuna suna ƙyamar abin da ba shi da kyau, gama an kafa kujerar sarauta ta wurin adalci ne.
The doing of wickedness is an abomination to kings; For by righteousness is the throne established.
13 Sarakuna sukan ji daɗi leɓuna masu yin gaskiya; sukan darjanta mutumin da yake faɗin gaskiya.
Righteous lips are the delight of kings, And they love him who speaketh right things.
14 Fushin sarki ɗan saƙon mutuwa ne, amma mai hikima yakan faranta masa rai.
The wrath of a king is messengers of death; But a wise man will pacify it.
15 Sa’ad da fuskar sarki ta haska, yana nufin rai ke nan; tagomashinsa yana kamar girgijen ruwa a bazara.
In the light of the king's countenance is life, And his favor is a like a cloud bringing the latter rain.
16 Ya ma fi kyau ka sami hikima fiye da zinariya, ka zaɓi fahimi a maimakon azurfa!
How much better is it to get wisdom than gold! Yea, to get understanding is rather to be chosen than silver.
17 Buɗaɗɗiyar hanyar masu aikata gaskiya kan guje wa mugunta; duk wanda yake lura da hanyarsa yakan lura da ransa.
It is the highway of the upright to depart from evil; He that taketh heed to his way preserveth his life.
18 Girmankai yakan zo kafin hallaka, girman kai yakan zo kafin fāɗuwa.
Pride goeth before destruction, And a haughty spirit before a fall.
19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu sauƙinkai, da ka raba ganima da masu girman kai.
Better is it to be of a humble spirit with the lowly, Than to share the spoil with the proud.
20 Duk wanda ya mai da hankali ga umarni yakan yi nasara, kuma mai albarka ne wanda yake dogara ga Ubangiji.
He who giveth heed to the word shall find good; And he who trusteth in the LORD, happy is he!
21 Akan ce da masu hikima a zuciya hazikai, kuma kalmomi masu daɗi kan inganta umarni.
The wise in heart shall be called intelligent, And sweetness of the lips increaseth learning.
22 Fahimi shi ne maɓulɓular rai ga waɗanda suke da shi, amma wauta kan kawo hukunci ga wawaye.
Understanding is a wellspring of life to him that hath it. And the chastisement of fools is their folly.
23 Zuciyar mai hikima kan bi da bakinsa, kuma leɓunansa kan inganta umarni.
The heart of the wise man instructeth his mouth, And addeth learning to his lips.
24 Kalmomi masu daɗi suna kama da kakin zuma, mai zaƙi ga rai da kuma warkarwa ga ƙasusuwa.
Pleasant words are like a honeycomb, Sweet to the taste, and health to the bones.
25 Akwai hanyar da ta yi kamar daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
There is a way that seemeth right to a man, But the end thereof is the way to death.
26 Marmarin cin abinci yakan yi wa ɗan ƙodago aiki; yunwarsa kan sa ya ci gaba.
The hunger of the laborer laboreth for him; For his mouth urgeth him on.
27 Mutumin banza yakan ƙulla mugunta, kuma jawabinsa yana kama da wuta mai ƙuna.
A worthless man diggeth mischief, And on his lips there is, as it were, a burning fire.
28 Fitinannen mutum yakan zuga tashin hankali, mai gulma kuma yakan raba abokai na kusa.
A deceitful man stirreth up strife, And a whisperer separateth friends.
29 Mutum mai tā-da-na-zaune-tsaye yakan ruɗi maƙwabcinsa ya kai shi a hanyar da ba ta da kyau.
A man of violence enticeth his neighbor, And leadeth him into a way which is not good.
30 Duk wanda ya ƙyifce da idonsa yana ƙulla maƙarƙashiya ce; duk wanda ya murguɗa leɓunansa yana niyya aikata mugunta ke nan.
He who shutteth his eyes to devise fraud, He who compresseth his lips, hath accomplished mischief!
31 Furfura rawani ne mai daraja; akan same ta ta wurin yin rayuwa ta adalci.
The hoary head is a crown of glory, If it be found in the way of righteousness.
32 Gara ka zama mai haƙuri da ka zama jarumi, ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
He who is slow to anger is better than the mighty; And he who ruleth his spirit, than he that taketh a city.
33 Akan jefa ƙuri’a a kan cinya, amma kowace shawara mai kyau daga Ubangiji ne.
The lot is cast into the lap; But the whole decision thereof is from the LORD.