< Karin Magana 14 >

1 Mace mai hikima kan gina gidanta, amma da hannunta wawiya takan rushe shi ƙasa.
A wise woman builds up her household. But a foolish one will pull down with her own hands what has been built up.
2 Wanda tafiyarsa ta aikata gaskiya ce kan ji tsoron Ubangiji, amma wanda hanyoyinsa ba a kan gaskiya ba ne yakan rena shi.
One who walks on a virtuous journey, and who fears God, is despised by him who advances along a disreputable way.
3 Maganar wawa kan kawo sanda a bayansa, amma leɓunan masu hikima kan tsare su.
In the mouth of the foolish, there is a rod of arrogance. But the lips of the wise guard them.
4 Inda ba shanu, wurin sa wa dabbobi abinci zai kasance ba kome, amma daga ƙarfin saniya ce yalwar girbi kan fito.
Where there are no oxen, the feeding trough is empty. But where there are many crops, there the strength of the ox is manifest.
5 Mashaidi na gaskiya ba ya ruɗu, amma mashaidin ƙarya kan baza ƙarairayi.
A faithful witness will not lie. But a deceitful witness offers a lie.
6 Mai ba’a kan nemi hikima amma ba ya samun kome, amma sani kan zo a sawwaƙe ga mai basira.
A mocker seeks wisdom and does not find it. The doctrine of the prudent is accessible.
7 Ka guji wawa, gama ba za ka sami sani a leɓunansa ba.
Go against a foolish man, and he does not acknowledge lips of prudence.
8 Hikima masu la’akari shi ne su yi tunani a kan hanyoyinsu, amma wautar wawaye ruɗu ne.
The wisdom of a discerning man is to understand his way. And the imprudence of the foolish is to be wandering astray.
9 Wawaye kan yi ba’a a gyaran zunubi, amma fatan alheri yana samuwa a cikin masu aikata gaskiya.
The foolish will speak mockingly of sin. But grace lingers among the just.
10 Kowace zuciya ta san ɓacin ranta, kuma babu wani dabam da zai yi rabon jin daɗinsa.
The heart that knows the bitterness of its own soul, in its gladness the outsider shall not meddle.
11 Za a rushe gidan mugu, amma tentin mai aikata gaskiya zai haɓaka.
The house of the impious will be wiped away. Yet truly, the tabernacles of the just shall spring forth.
12 Akwai hanyar da ta yi kamar tana daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
There is a way which seems just to a man, but its conclusion leads to death.
13 Ko cikin dariya zuciya takan yi ciwo, kuma farin ciki kan iya ƙarasa a baƙin ciki.
Laughter shall be mingled with sorrow, and mourning occupies the limits of joy.
14 Marasa bangaskiya za su sami sakamako cikakke saboda hanyoyinsu, kuma mutumin kirki zai sami lada saboda nasa.
The foolish will be filled up by his own ways. And the good man shall be above him.
15 Marar azanci kan gaskata kome, amma mai la’akari kan yi tunani game da matakinsa.
The innocent trust every word. The astute one considers his own steps. Nothing good will be for the deceitful son. But the wise servant shall act prosperously and his way will be set in order.
16 Mai hikima kan ji tsoron Ubangiji ya kuma guji mugunta, amma wawa yana da girman kai yakan yi kome da garaje.
The wise fear, and so turn away from evil. The foolish leap ahead with confidence.
17 Mutum mai saurin fushi yakan yi ayyukan wauta, akan kuma ƙi mai son nuna wayo.
The impatient will work foolishness. And a resourceful man is hated.
18 Marar azanci kan gāji wauta, amma mai la’akari kan sami rawanin sani.
The childish will possess foolishness, and the discerning will anticipate knowledge.
19 Masu mugunta za su rusuna a gaban masu kirki, mugaye kuma za su yi haka a ƙofofin adalai.
The evil will fall down before the good. And the impious will fall down before the gates of the just.
20 Maƙwabta sukan gudu daga matalauta, amma masu arziki suna da abokai da yawa.
The pauper will be hated, even by his own neighbor. Yet truly, the friends of the wealthy are many.
21 Duk wanda ya rena maƙwabci ya yi zunubi, amma mai albarka ne wanda yake alheri ga mabukata.
Whoever despises his neighbor, sins. But whoever pities the poor shall be blessed. Whoever trusts in the Lord loves mercy.
22 Ba waɗanda suke ƙulla mugunta sukan kauce ba? Amma waɗanda suke ƙulla abin da yake mai kyau sukan sami ƙauna da aminci.
They wander astray who work evil. But mercy and truth prepare good things.
23 Duk aiki tuƙuru yakan kawo riba, amma zama kana surutu kan kai ga talauci kawai.
In every work, there shall be abundance. But where there are many words, there is often need.
24 Dukiyar masu hikima ita ce rawaninsu, amma wautar wawaye kan haifar da wauta ne kawai.
The crown of the wise is their wealth. The senselessness of the foolish is imprudence.
25 Mashaidin gaskiya kan ceci rayuka, amma mashaidin ƙarya mai ruɗu ne.
A faithful witness frees souls. And the chameleon utters lies.
26 Duk mai tsoron Ubangiji yana da zaunannen mafaka, kuma ga’ya’yansa zai zama mafaka.
In the fear of the Lord is the faithfulness of strength, and there shall be hope for his sons.
27 Tsoron Ubangiji shi ne maɓulɓular rai yakan juye mutum daga tarkon mutuwa.
The fear of the Lord is a fountain of life, so as to turn aside from the ruin of death.
28 Yawan mutane shi ne ɗaukakar sarki, amma in ba tare da mabiya ba sarki ba kome ba ne.
In a multitude of people, there is dignity for the king. And in a paucity of people, there is disgrace for the prince.
29 Mutum mai haƙuri yana da fahimi mai yawa, amma mai saurin fushi yakan nuna wautarsa a fili.
Whoever is patient is governed by much prudence. But whoever is impatient exalts his foolishness.
30 Zuciya mai salama kan ba jiki rai, amma kishi kan sa ƙasusuwa su yi ciwo.
The well-being of the heart is life for the flesh. But envy is decay for the bones.
31 Duk wanda ya zalunci matalauci ya zagi Mahaliccinsu ke nan, amma duk wanda ya yi alheri ga mabukata yana girmama Allah ne.
Whoever slanders the indigent argues against his Maker. But he who has compassion on the poor honors his Maker.
32 Sa’ad bala’i ya auku, mugaye kan fāɗi, amma ko a mutuwa masu adalci suna da mafaka.
The impious will be expelled in his malice. But the just finds hope even in his own death.
33 Hikima tana a zuciyar mai azanci, kuma ko a cikin wawaye takan sa a santa.
In the heart of the prudent, wisdom finds rest. And so shall he instruct all the uneducated.
34 Adalci yakan ɗaukaka al’umma, amma zunubi kan kawo kunya ga kowane mutane.
Justice elevates a nation. But sin makes the peoples miserable.
35 Sarki yakan yi murna a kan bawa mai hikima, amma bawa marar kunya kan jawo fushinsa.
An intelligent minister is acceptable to the king. Whoever is useless shall bear his wrath.

< Karin Magana 14 >