< Karin Magana 14 >
1 Mace mai hikima kan gina gidanta, amma da hannunta wawiya takan rushe shi ƙasa.
Kvinders Visdom har bygget sit Hus; men Daarskaben bryder det ned med sine Hænder.
2 Wanda tafiyarsa ta aikata gaskiya ce kan ji tsoron Ubangiji, amma wanda hanyoyinsa ba a kan gaskiya ba ne yakan rena shi.
Den, som vandrer i sin Oprigtighed, frygter Herren; men den, som gaar paa Krogveje, foragter ham.
3 Maganar wawa kan kawo sanda a bayansa, amma leɓunan masu hikima kan tsare su.
I Daarens Mund er Hovmods Ris; men de vises Læber skulle bevare dem selv.
4 Inda ba shanu, wurin sa wa dabbobi abinci zai kasance ba kome, amma daga ƙarfin saniya ce yalwar girbi kan fito.
Hvor ingen Øksne ere, der er Krybben ren; men megen Indtægt kommer ved Oksens Kraft.
5 Mashaidi na gaskiya ba ya ruɗu, amma mashaidin ƙarya kan baza ƙarairayi.
Et trofast Vidne lyver ikke; men et falsk Vidne udblæser Løgne.
6 Mai ba’a kan nemi hikima amma ba ya samun kome, amma sani kan zo a sawwaƙe ga mai basira.
Spotteren søger Visdom, og han finder den ikke; men for den forstandige er Kundskab let.
7 Ka guji wawa, gama ba za ka sami sani a leɓunansa ba.
Gak bort fra en Mand, som er en Daare; thi du vil ikke have fundet Kundskab paa hans Læber.
8 Hikima masu la’akari shi ne su yi tunani a kan hanyoyinsu, amma wautar wawaye ruɗu ne.
Den kloges Visdom er, at han forstaar sig paa sin Vej; men Daarers Taabelighed er, at de blive bedragne.
9 Wawaye kan yi ba’a a gyaran zunubi, amma fatan alheri yana samuwa a cikin masu aikata gaskiya.
Daarerne spottes af deres eget Skyldoffer; men med de oprigtige er Velbehageligheden.
10 Kowace zuciya ta san ɓacin ranta, kuma babu wani dabam da zai yi rabon jin daɗinsa.
Hjertet kender sin Sjæls Bitterhed, og en fremmed skal ikke blande sig i dets Glæde.
11 Za a rushe gidan mugu, amma tentin mai aikata gaskiya zai haɓaka.
De ugudeliges Hus skal ødelægges; men de retsindiges Telt skal blomstre.
12 Akwai hanyar da ta yi kamar tana daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
Der er en Vej, som kan synes en Mand ret; men til sidst bliver den Vej til Døden.
13 Ko cikin dariya zuciya takan yi ciwo, kuma farin ciki kan iya ƙarasa a baƙin ciki.
Selv under Latteren føler Hjertet Smerte, og til sidst bliver Glæden Bedrøvelse.
14 Marasa bangaskiya za su sami sakamako cikakke saboda hanyoyinsu, kuma mutumin kirki zai sami lada saboda nasa.
Den, hvis Hjerte er afveget, skal mættes ved sine Veje, men den gode Mand ved det, han har i Eje.
15 Marar azanci kan gaskata kome, amma mai la’akari kan yi tunani game da matakinsa.
Den uerfarne tror alting, men den kloge agter paa sin Gang.
16 Mai hikima kan ji tsoron Ubangiji ya kuma guji mugunta, amma wawa yana da girman kai yakan yi kome da garaje.
Den vise frygter og viger fra ondt; men en Daare er overmodig, og tryg.
17 Mutum mai saurin fushi yakan yi ayyukan wauta, akan kuma ƙi mai son nuna wayo.
Den, som er hastig til Vrede, gør Daarlighed, og den underfundige Mand hades.
18 Marar azanci kan gāji wauta, amma mai la’akari kan sami rawanin sani.
De uvidende arve Daarlighed; men de kloge favne Kundskab.
19 Masu mugunta za su rusuna a gaban masu kirki, mugaye kuma za su yi haka a ƙofofin adalai.
De onde maa bøje sig for de godes Ansigt og de ugudelige for den retfærdiges Porte.
20 Maƙwabta sukan gudu daga matalauta, amma masu arziki suna da abokai da yawa.
Selv for sin Ven er den fattige forhadt; men mange ere de, som elske den rige.
21 Duk wanda ya rena maƙwabci ya yi zunubi, amma mai albarka ne wanda yake alheri ga mabukata.
Hvo som foragter sin Næste, synder; men den, som forbarmer sig over de elendige, er lyksalig.
22 Ba waɗanda suke ƙulla mugunta sukan kauce ba? Amma waɗanda suke ƙulla abin da yake mai kyau sukan sami ƙauna da aminci.
Fare ikke de vild, som optænke ondt? men de, som optænke godt, finde Miskundhed og Troskab.
23 Duk aiki tuƙuru yakan kawo riba, amma zama kana surutu kan kai ga talauci kawai.
I alt besværligt Arbejde er der Fordel; men hvor det bliver ved Læbers Ord, fører det kun til Mangel.
24 Dukiyar masu hikima ita ce rawaninsu, amma wautar wawaye kan haifar da wauta ne kawai.
De vises Rigdom er deres Krone; men Daarers Taabelighed bliver Taabelighed.
25 Mashaidin gaskiya kan ceci rayuka, amma mashaidin ƙarya mai ruɗu ne.
Et sanddru Vidne redder Sjæle, men den, som udblæser Løgn, er svigefuld.
26 Duk mai tsoron Ubangiji yana da zaunannen mafaka, kuma ga’ya’yansa zai zama mafaka.
I Herrens Frygt har en et stærkt Værn, og for hans Børn skal der være en Tilflugt.
27 Tsoron Ubangiji shi ne maɓulɓular rai yakan juye mutum daga tarkon mutuwa.
Herrens Frygt er Livets Kilde, saa at man viger fra Dødens Snarer.
28 Yawan mutane shi ne ɗaukakar sarki, amma in ba tare da mabiya ba sarki ba kome ba ne.
At have meget Folk er en Konges Ære; men hvor Folket er borte, er det en Fyrstes Fordærvelse.
29 Mutum mai haƙuri yana da fahimi mai yawa, amma mai saurin fushi yakan nuna wautarsa a fili.
Den langmodige har megen Forstand; men den, som er hastig i Sindet, forraader Daarskab.
30 Zuciya mai salama kan ba jiki rai, amma kishi kan sa ƙasusuwa su yi ciwo.
Et blidt Hjerte er Liv for Legemet; men Hidsighed er Raaddenhed for Benene,
31 Duk wanda ya zalunci matalauci ya zagi Mahaliccinsu ke nan, amma duk wanda ya yi alheri ga mabukata yana girmama Allah ne.
Hvo som fortrykker den ringe, forhaaner hans Skaber; men hvo som forbarmer sig over den fattige, ærer ham.
32 Sa’ad bala’i ya auku, mugaye kan fāɗi, amma ko a mutuwa masu adalci suna da mafaka.
Den ugudelige styrtes for sin Ondskab; men den retfærdige har Fortrøstning i sin Død.
33 Hikima tana a zuciyar mai azanci, kuma ko a cikin wawaye takan sa a santa.
I den forstandiges Hjerte hviler Visdommen; men i Daarers Indre giver den sig til Kende.
34 Adalci yakan ɗaukaka al’umma, amma zunubi kan kawo kunya ga kowane mutane.
Retfærdighed ophøjer et Folk; men Synden er Folkenes Skændsel
35 Sarki yakan yi murna a kan bawa mai hikima, amma bawa marar kunya kan jawo fushinsa.
Kongens Velbehag er til en klog Tjener, men hans Vrede er over den, som gør Skam.