< Karin Magana 11 >
1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
EL peso falso abominación es á Jehová: mas la pesa cabal le agrada.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
Cuando viene la soberbia, viene también la deshonra: mas con los humildes es la sabiduría.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
La integridad de los rectos los encaminará: mas destruirá á los pecadores la perversidad de ellos.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
No aprovecharán las riquezas en el día de la ira: mas la justicia librará de muerte.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
La justicia del perfecto enderezará su camino: mas el impío por su impiedad caerá.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
La justicia de los rectos los librará: mas los pecadores en su pecado serán presos.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
Cuando muere el hombre impío, perece [su] esperanza; y la espectativa de los malos perecerá.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
El justo es librado de la tribulación: mas el impío viene en lugar suyo.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
El hipócrita con la boca daña á su prójimo: mas los justos son librados con la sabiduría.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
En el bien de los justos la ciudad se alegra: mas cuando los impíos perecen, hay fiestas.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
Por la bendición de los rectos la ciudad será engrandecida: mas por la boca de los impíos ella será trastornada.
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
El que carece de entendimiento, menosprecia á su prójimo: mas el hombre prudente calla.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
El que anda en chismes, descubre el secreto: mas el de espíritu fiel encubre la cosa.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
Cuando faltaren las industrias, caerá el pueblo: mas en la multitud de consejeros hay salud.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
Con ansiedad será afligido el que fiare al extraño: mas el que aborreciere las fianzas [vivirá] confiado.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
La mujer graciosa tendrá honra: y los fuertes tendrán riquezas.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
A su alma hace bien el hombre misericordioso: mas el cruel atormenta su carne.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
El impío hace obra falsa: mas el que sembrare justicia, tendrá galardón firme.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
Como la justicia [es] para vida, así el que sigue el mal [es] para su muerte.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
Abominación son á Jehová los perversos de corazón: mas los perfectos de camino le son agradables.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
[Aunque llegue] la mano á la mano, el malo no quedará sin castigo: mas la simiente de los justos escapará.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
Zarcillo de oro en la nariz del puerco, [es] la mujer hermosa y apartada de razón.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
El deseo de los justos es solamente bien: [mas] la esperanza de los impíos es enojo.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
Hay quienes reparten, y les es añadido más: y hay quienes son escasos más de lo que es justo, mas vienen á pobreza.
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
El alma liberal será engordada: y el que saciare, él también será saciado.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
Al que retiene el grano, el pueblo lo maldecirá: mas bendición será sobre la cabeza del que vende.
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
El que madruga al bien, buscará favor: mas el que busca el mal, vendrále.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
El que confía en sus riquezas, caerá: mas los justos reverdecerán como ramos.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
El que turba su casa heredará viento; y el necio será siervo del sabio de corazón.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
El fruto del justo es árbol de vida: y el que prende almas, es sabio.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
Ciertamente el justo será pagado en la tierra: ¡cuánto más el impío y el pecador!