< Karin Magana 11 >
1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
Лажна су мерила мрска Господу, а права мера угодна Му је.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
Кад дође охолост, дође и срамота; а у смерних је мудрост.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
Праведне води безазленост њихова, а безаконике сатире злоћа њихова.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
Неће помоћи богатство у дан гнева, а правда избавља од смрти.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
Правда безазленога управља пут његов, а безбожник пада од своје безбожности.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
Праведне избавља правда њихова, а безаконици хватају се у својој злоћи.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
Кад умире безбожник, пропада надање, и најјаче уздање пропада.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
Праведник се избавља из невоље, а безбожник долази на његово место.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
Лицемер квари устима ближњег свог; али се праведници избављају знањем.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
Добру праведних радује се град; а кад пропадају безбожници, бива певање.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
Благословима праведних људи подиже се град, а с уста безбожничких раскопава се.
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
Безумник се руга ближњему свом, а разуман човек ћути.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
Опадач тумарајући издаје тајну; а ко је верна срца, таји ствар.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
Где нема савета, пропада народ, а помоћ је у мноштву саветника.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
Зло пролази ко се јамчи за туђина; а ко мрзи на јамство, без бриге је.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
Жена мила добија част, а силни добијају богатство.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
Милостив човек чини добро души својој, а немилостив уди свом телу.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
Безбожни ради посао преваран; а ко сеје правду, поуздана му је плата.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
Ко се држи правде, на живот му је; а ко иде за злом, на смрт му је.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
Мрски су Господу који су опаког срца; а мили су Му који су безазлени на свом путу.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
Зао човек неће остати без кара ако и друге узме у помоћ; а семе праведних избавиће се.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
Жена лепа а без разума златна је брњица у губици свињи.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
Жеља је праведних само добро, а очекивање безбожних гнев.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
Један просипа, и све више има; а други тврдује сувише, и све је сиромашнији.
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
Подашна рука бива богатија, и ко напаја, сам ће бити напојен.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
Ко не да жита, проклиње га народ, а ко продаје, благослов му је над главом.
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
Ко тражи добро, добија љубав; а ко тражи зло, задесиће га.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
Ко се узда у богатство своје, пропашће; а праведници ће се као грана зеленети.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
Ко затире кућу своју, наследиће ветар; и безумник ће служити мудром.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
Плод је праведников дрво животно, и мудри обучава душе.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
Гле, праведнику се на земљи плаћа, а камоли безбожнику и грешнику?