< Karin Magana 11 >

1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
Une fausse balance est une abomination pour Yahvé, mais les poids précis sont sa spécialité.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
Quand vient l'orgueil, vient ensuite la honte, mais avec l'humilité vient la sagesse.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
L'intégrité des hommes intègres les guidera, mais la perversité des perfides les détruira.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
Les richesses ne profitent pas au jour de la colère, mais la justice délivre de la mort.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
La justice de l'irréprochable dirigera son chemin, mais le méchant tombera par sa propre méchanceté.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
La justice des hommes intègres les délivrera, mais les infidèles seront piégés par de mauvais désirs.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
Quand un méchant meurt, l'espoir périt, et l'attente du pouvoir n'aboutit à rien.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
Le juste est délivré de la détresse, et le méchant prend sa place.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
De sa bouche, l'impie détruit son prochain, mais les justes seront délivrés par la connaissance.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
Quand tout va bien pour le juste, la ville se réjouit. Quand les méchants périssent, il y a des cris.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
Par la bénédiction des hommes droits, la ville est exaltée, mais elle est renversée par la bouche des méchants.
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
Celui qui méprise son prochain est dépourvu de sagesse, mais un homme compréhensif garde sa paix.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
Celui qui apporte des ragots trahit une confiance, mais celui qui est d'un esprit digne de confiance est celui qui garde un secret.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
Là où il n'y a pas de direction sage, la nation tombe, mais dans la multitude des conseillers il y a la victoire.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
Celui qui se porte garant pour un étranger en souffrira, mais celui qui refuse les gages de garantie est en sécurité.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
Une femme gracieuse obtient l'honneur, mais les hommes violents obtiennent des richesses.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
L'homme miséricordieux fait du bien à son âme, mais celui qui est cruel trouble sa propre chair.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
Les méchants gagnent un salaire trompeur, mais celui qui sème la justice récolte une récompense sûre.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
Celui qui est vraiment juste obtient la vie. Celui qui poursuit le mal obtient la mort.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
Ceux qui ont le cœur pervers sont en abomination à Yahvé, mais ceux dont les voies sont irréprochables font ses délices.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
Très certainement, le méchant ne restera pas impuni, mais la progéniture des justes sera délivrée.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
Comme un anneau d'or dans le groin d'un porc, est une belle femme qui manque de discrétion.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
Le désir des justes n'est que du bien. L'attente des méchants est la colère.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
Il y en a un qui disperse, et qui augmente encore. Il y a celui qui retient plus qu'il ne faut, mais qui gagne la pauvreté.
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
L'âme libérale sera engraissée. Celui qui arrose sera lui-même arrosé.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
Les gens maudissent celui qui retient le grain, mais la bénédiction sera sur la tête de celui qui le vend.
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
Celui qui cherche diligemment le bien cherche la faveur, mais celui qui cherche le mal, le mal viendra à lui.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
Celui qui se confie en ses richesses tombera, mais le juste fleurira comme la feuille verte.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
Celui qui trouble sa propre maison héritera du vent. Les insensés seront les serviteurs des sages de cœur.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
Le fruit du juste est un arbre de vie. Celui qui est sage gagne des âmes.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
Voici, les justes seront remboursés sur la terre, combien plus le méchant et le pécheur!

< Karin Magana 11 >