< Karin Magana 11 >

1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
Yahweh detests [people who use] scales that do not weigh correctly; he is delighted with [those who use] correct weights on the scales.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
[People who are] proud will [eventually] be disgraced; it is wise to be humble.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
[People who are] good are guided by [doing what is] honest; those who are not honest will be ruined because of the wrong things that they do.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
[Your] money will not help [you] on the day that [God] judges [and punishes people]; but if you live righteously, you will live a long time.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
When people are honest and good, that will (direct their paths/show them what is right for them to do); but wicked [people will] experience disasters because of the evil things that they do.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
[God] rescues/protects righteous [people] because they (are honest/do what is right), but those who (are treacherous/cannot be trusted) will be trapped because of their being greedy.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
When wicked [people] die, they cannot confidently expect to receive anything [that is good]; they expect that [their money] will help/save them, but it will not.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
[Yahweh] rescues righteous [people] from their troubles/difficulties; instead, it is the wicked who will have troubles.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
Godless people can ruin others by what they say [MTY], but righteous [people will] be saved by [their (own] good sense/being wise).
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
When things go well for righteous [people], [the people in] [MTY] their city are happy, and they shout joyfully when wicked [people] die.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
When righteous [people request God to] bless a city, that city will become great, but cities are ruined by what wicked [people] say [MTY].
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
It is foolish to despise others; those who (have good sense/are wise) do not say anything [to criticize others].
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
Those who (spread gossip/tell bad things about others) will tell your secrets [to others], but if there is someone whom you can trust, you can trust him to not tell your secrets [to others].
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
A nation will be destroyed/ruined if it does not have [leaders] who guide it [wisely]; but if there are many [good] advisors, the nation remains secure.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
If you promise a stranger that you will pay his debt [if he cannot pay it himself], you will regret it. You will be safe if you refuse to guarantee that you will pay someone else’s debts.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
[People] honor/respect women who are kind/gracious; ruthless/violent people may get a lot of money, [but that is all that they will get].
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
Those who are kind benefit themselves [because others will be kind to them], but those who are cruel will hurt themselves [because others will be cruel to them].
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
If wicked people earn a lot of money, that will deceive them [because they will not keep it for very long], but those who do what is right will surely be rewarded [by God forever].
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
Those who always do what is right will live [a long/happy life], but those who insist on doing what is wrong will not live [very long].
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
Yahweh hates those who are always thinking about doing evil things, but he is delighted with those who always do what is right.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
It is certain that [Yahweh] will punish evil people and that righteous people will escape [from being punished].
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
[It is] ([unsuitable/not proper/disgusting]) for a beautiful woman not to know what is right to do, like [SIM] [it is unsuitable/disgusting] for a pig to have a gold ring in its snout/nose.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
When the things that righteous people want happen, it brings good [to them and to others], but when the wicked get what they want, it causes everyone else to become angry.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
Some people give [their money] generously [to poor people], but they become richer [in spite of that], and some people hold tightly to their money, but they still become poor [in spite of that].
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
Those who give generously [to others] will prosper; if you help others, [they/someone] will help you, too.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
People curse/despise someone who hoards his grain [and does not sell it], waiting to get a higher/bigger price for it, but they praise someone who sells it [when people need it, even when the price is not high].
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
If you sincerely want to [do what is] right, [people] will respect you, but if you are wanting to cause trouble, trouble is what you will get.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
Those who trust in their money will [disappear like the] withered [leaves that fall from the trees], but righteous [people] will keep going strong, like green leaves [in the summer].
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
Those who bring troubles to their families will inherit nothing [MET] [from them], and those who do foolish things [like that] will [some day] become the servants of wise [people].
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
Those who live righteously will live [for a long time], but [those who act] violently will destroy [their own] lives (OR, those who are wise will have many people come and live with them).
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
[Sometimes] righteous [people] are rewarded [here] on the earth, but it is much more certain that very wicked people [DOU] [will be rewarded by being punished].

< Karin Magana 11 >