< Karin Magana 11 >
1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
A false balance [is] abomination to the LORD: but a just weight [is] his delight.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
[When] pride cometh, then cometh shame: but with the lowly [is] wisdom.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
The integrity of the upright shall guide them: but the perverseness of transgressors shall destroy them.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
Riches profit not in the day of wrath: but righteousness delivereth from death.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
The righteousness of the perfect shall direct his way: but the wicked shall fall by his own wickedness.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
The righteousness of the upright shall deliver them: but transgressors shall be taken in [their own] naughtiness.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
When a wicked man dieth, [his] expectation shall perish: and the hope of unjust [men] perisheth.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
The righteous is delivered out of trouble, and the wicked cometh in his stead.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
An hypocrite with [his] mouth destroyeth his neighbour: but through knowledge shall the just be delivered.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
When it goeth well with the righteous, the city rejoiceth: and when the wicked perish, [there is] shouting.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
By the blessing of the upright the city is exalted: but it is overthrown by the mouth of the wicked.
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
He that is void of wisdom despiseth his neighbour: but a man of understanding holdeth his peace.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
A talebearer revealeth secrets: but he that is of a faithful spirit concealeth the matter.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
Where no counsel [is], the people fall: but in the multitude of counsellors [there is] safety.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
He that is surety for a stranger shall smart [for it: ] and he that hateth suretiship is sure.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
A gracious woman retaineth honour: and strong [men] retain riches.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
The merciful man doeth good to his own soul: but [he that is] cruel troubleth his own flesh.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
The wicked worketh a deceitful work: but to him that soweth righteousness [shall be] a sure reward.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
As righteousness [tendeth] to life: so he that pursueth evil [pursueth it] to his own death.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
They that are of a froward heart [are] abomination to the LORD: but [such as are] upright in [their] way [are] his delight.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
[Though] hand [join] in hand, the wicked shall not be unpunished: but the seed of the righteous shall be delivered.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
[As] a jewel of gold in a swine’s snout, [so is] a fair woman which is without discretion.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
The desire of the righteous [is] only good: [but] the expectation of the wicked [is] wrath.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
There is that scattereth, and yet increaseth; and [there is] that withholdeth more than is meet, but [it tendeth] to poverty.
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
The liberal soul shall be made fat: and he that watereth shall be watered also himself.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
He that withholdeth corn, the people shall curse him: but blessing [shall be] upon the head of him that selleth [it].
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
He that diligently seeketh good procureth favour: but he that seeketh mischief, it shall come unto him.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
He that trusteth in his riches shall fall: but the righteous shall flourish as a branch.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
He that troubleth his own house shall inherit the wind: and the fool [shall be] servant to the wise of heart.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
The fruit of the righteous [is] a tree of life; and he that winneth souls [is] wise.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
Behold, the righteous shall be recompensed in the earth: much more the wicked and the sinner.