< Karin Magana 11 >

1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
A deceitful balance is an abomination before the Lord: and a just weight is his will.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
Where pride is, there also shall be reproach: but where humility is, there also is wisdom.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
The simplicity of the just shall guide them: and the deceitfulness of the wicked shall destroy them.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
Riches shall not profit in the day of revenge: but justice shall deliver from death.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
The justice of the upright shall make his way prosperous: and the wicked man shall fall by his own wickedness.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
The justice of the righteous shall deliver them: and the unjust shall be caught in their own snares.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
When the wicked man is dead, there shall be no hope any more: and the expectation of the solicitous shall perish.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
The just is delivered out of distress: and the wicked shall be given up for him.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
The dissembler with his mouth deceiveth his friend: but the just shall be delivered by knowledge.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
When it goeth well with the just the city shall rejoice: and when the wicked perish there shall be praise.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
By the blessing of the just the city shall be exalted: and by the mouth of the wicked it shall be overthrown.
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
He that despiseth his friend, is mean of heart: but the wise man will hold his peace.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
He that walketh deceitfully, revealeth secrets: but he that is faithful, concealeth the thing committed to him by his friend.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
Where there is no governor, the people shall fall: but there is safety where there is much counsel.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
He shall be afflicted with evil, that is surety for a stranger: but he that is aware of the snares, shall be secure.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
A gracious woman shall find glory: and the strong shall have riches.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
A merciful man doth good to his own soul: but he that is cruel casteth off even his own kindred.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
The wicked maketh an unsteady work: but to him that soweth justice, there is a faithful reward.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
Clemency prepareth life: and the pursuing of evil things, death.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
A perverse heart is abominable to the Lord: and his will is in them that walk sincerely.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
Hand in hand the evil man shall not be innocent: but the seed of the just shall be saved.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
A golden ring in a swine’s snout, a woman fair and foolish.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
The desire of the just is all good: the expectation of the wicked is indignation.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
Some distribute their own goods, and grow richer: others take away what is not their own, and are always in want.
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
The soul which blesseth, shall be made fat: and he that inebriateth, shall be inebriated also himself.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
He that hideth up corn, shall be cursed among the people: but a blessing upon the head of them that sell.
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
Well doth he rise early who seeketh good things; but he that seeketh after evil things shall be oppressed by them.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
He that trusteth in his riches shall fall: but the just shall spring up as a green leaf.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
He that troubleth his own house, shall inherit the winds: and the fool shall serve the wise.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
The fruit of the just man is a tree of life: and he that gaineth souls, is wise.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
If the just man receive in the earth, how much more the wicked and the sinner.

< Karin Magana 11 >