< Karin Magana 11 >

1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
False balances are an abomination before the Lord: but a just weight is acceptable unto him.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
Wherever pride enters, there will be also disgrace: but the mouth of the lowly meditates wisdom.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
When a just man dies he leaves regret: but the destruction of the ungodly is speedy, and causes joy.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
[Possessions will not profit in a day of wrath, but righteousness will deliver from death. ]
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
Righteousness traces out blameless paths: but ungodliness encounters unjust dealing.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
The righteousness of upright men delivers them: but transgressors are caught in their own destruction.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
At the death of a just man his hope does not perish: but the boast of the ungodly perishes.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
A righteous man escapes from a snare, and the ungodly man is delivered up in his place.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
In the mouth of ungodly men is a snare to citizens: but the understanding of righteous men is prosperous.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
In the prosperity of righteous men a city prospers: but by the mouth of ungodly men it is overthrown.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
[At the blessing of the upright a city shall be exalted. ]
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
A man void of understanding sneers at [his fellow] citizens: but a sensible man is quiet.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
A double-tongued man discloses the [secret] counsels of an assembly: but he that is faithful in spirit conceals matters.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
They that have no guidance fall like leaves: but in much counsel there is safety.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
A bad man does harm wherever he meets a just man: and he hates the sound of safety.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
A gracious wife brings glory to her husband: but a woman hating righteousness is a theme of dishonour. The slothful come to want: but the diligent support themselves with wealth.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
A merciful man does good to his own soul: but the merciless destroys his own body.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
An ungodly man performs unrighteous works: but the seed of the righteous is a reward of truth.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
A righteous son is born for life: but the persecution of the ungodly [ends] in death.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
Perverse ways are an abomination to the Lord: but all they that are blameless in their ways are acceptable to him.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
He that unjustly strikes hands shall not be unpunished: but he that sows righteousness he shall receive a faithful reward.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
As an ornament in a swine's snout, so is beauty to an ill-minded women.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
All the desire of the righteous is good: but the hope of the ungodly shall perish.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
There are [some] who scatter their own, and make it more: and there are [some] also who gather, [yet] have less.
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
Every sincere soul is blessed: but a passionate man is not graceful.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
May he that hoards corn leave it to the nation: but blessing be on the head of him that gives [it].
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
He that devises good [counsels] seeks good favour: but [as for] him that seeks after evil, [evil] shall overtake him.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
He that trusts in wealth shall fall; but he that helps righteous men shall rise.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
He that deals not graciously with his own house shall inherit the wind; and the fool shall be servant to the wise man.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
Out of the fruit of righteousness grows a tree of life; but the souls of transgressors are cut off before their time.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
If the righteous scarcely be saved, where shall the ungodly and the sinner appear?

< Karin Magana 11 >