< Karin Magana 11 >
1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
Неточни везни са мерзост Господу; А точни грамове са угодни Нему.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
Дойде ли гордост, дохожда и срам. А мъдростта е със смирените.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
Незлобието на справедливите ще ги ръководи, А извратеността на коварните ще ги погуби.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
В ден на гняв богатството не ползува, А правдата избавя от смърт.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
Правдата на непорочния ще оправя пътя му, А нечестивият ще падне чрез своето нечестие.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
Правдата на справедливите ще ги избави, А коварните ще се хванат в злобата си.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
Като умира нечестивият, ожиданото от него загива; Така загива надеждата на насилниците.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
Праведният се отървава от беда, А вместо него изпада в нея нечестивият.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
Безбожният погубва ближния си с устата си. Но чрез знанието на праведните ще се избави.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
Когато благоденствуват праведните, градът се весели; И когато погиват нечестивите става тържество.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
Чрез благословението върху праведните градът се въздига, А чрез устата на нечестивите се съсипва.
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
Който презира ближния си е скудоумен; А благоразумният човек мълчи.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
Одумникът обхожда и открива тайните, А верният духом потайва работата.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
Дето няма мъдро ръководене народът пропада, А в многото съветници има безопасност.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
Който поръчителствува за чужд човек, зле ще пострада, А който мрази поръчителството е в безопасност.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
Благодатната жена придобива чест; И насилниците придобиват богатство.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
Милостивият човек струва добро на себе си, А жестокият смущава своето тяло.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
Нечестивият придобива измамлива печалба, А който сее правда има сигурна награда.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
Който е утвърден в правдата, ще стане живот, А който се стреми към злото съдействува за своята смърт.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
Развратените в сърце са мерзост Господу, А непорочните в пътя си са угодни Нему,
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
Даже ръка с ръка да се съедини пак нечестивият няма да остане ненаказан., А потомството на праведните ще се избави.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
Както е златна халка на носа на свиня, Така е красивата, но безразсъдна жена.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
Желаното от праведните е само добро, А ожиданото от нечестивите е надменност.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
Един разпръсва щедро, но пак има повече изобилие, А друг се скъпи без мяра, но пак стига до немотия,
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
Благотворната душа ще бъде наситена; И който пои, сам ще бъде напоен.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
Който задържа жито ще бъде прокълнат от народа, А който продава, благословение ще почива на главата му.
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
Който усърдно търси доброто, търси и благоволение, А който търси злото, то ще дойде и върху него.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
Който уповава на богатството си, ще падне, А праведните ще цъфтят като зелен лист.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
Който смущава своя си дом ще наследи вятър; И безумният ще стане слуга на мъдрия по сърце.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
Плодът на праведния е дърво на живот; И който е мъдър придобива души.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
Ето, и на праведния се въздава на земята, - Колко повече на нечестивия и на грешния!