< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Proverbios de Salomón, hijo de David, rey de Israel:
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
para aprender sabiduría e instrucción, para entender las palabras sensatas;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
para instruirse en la sabiduría, en la justicia, equidad y rectitud;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
para enseñar discernimiento a los sencillos, y a los jóvenes conocimientos y discreción.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Escuche el sabio y acrecerá en saber. El hombre inteligente adquirirá maestría
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
en entender las parábolas y su sentido misterioso, las sentencias de los sabios y sus enigmas.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
El temor de Yahvé es el principio de la sabiduría; solo los insensatos desprecian la sabiduría y la doctrina.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Escucha, hijo mío, la instrucción de tu padre; y no deseches las enseñanzas de tu madre.
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
Serán una corona de gracia para tu cabeza, un collar para tu cuello.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Hijo mío, si los malvados quieren seducirte, no les des oído;
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
si te dicen: “Ven con nosotros; pongamos asechanzas a la vida ajena, tendamos por mero antojo celadas al inocente;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
traguémoslos vivos, como el sepulcro, enteros, como los que descienden a la fosa; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
y hallaremos preciosas riquezas, henchiremos de despojos nuestras casas.
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Echa tu suerte con nosotros; sea una sola la bolsa de todos nosotros.”
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Hijo mío, no sigas sus caminos; aparta tu pie de sus senderos;
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
porque sus pies corren al mal, van presurosos a derramar sangre.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
En vano se tiende la red ante los ojos de los pájaros;
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
mas ellos arman asechanzas a su propia sangre, traman maquinaciones contra su propia vida.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Tal es la senda de los codiciosos de ganancia, quita la vida a los propios dueños.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
La sabiduría clama en las calles, en las plazas levanta su voz;
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
llama donde hay más concurso de gente, en las puertas de la ciudad expone su doctrina:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
¿Hasta cuándo, oh necios, amaréis la necedad? ¿Hasta cuándo los burladores se deleitarán en burlas, y odiarán los fatuos la sabiduría?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Volveos para (oír) mi instrucción, y derramaré sobre vosotros mi espíritu, quiero enseñaros mis palabras.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Os convidé y no respondisteis, tendí mis manos, y nadie prestó atención;
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
rechazasteis todos mis consejos, y ningún caso hicisteis de mis amonestaciones.
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
Por eso también yo me reiré de vuestra calamidad, y me burlaré cuando os sobrevenga el espanto,
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
cuando os sobrevenga cual huracán el terror, cuando caiga sobre vosotros, como torbellino, la calamidad, y os acometan la angustia y la tribulación.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Entonces me llamarán, y no les responderé; madrugarán a buscarme, y no me hallarán,
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
por cuanto aborrecieron la instrucción y abandonaron el temor de Dios,
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
no amando mi consejo, y desdeñando mis exhortaciones.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Comerán los frutos de su conducta, y se saciarán de sus propios consejos.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Porque la indocilidad lleva a los necios a la muerte, y la prosperidad de los insensatos es causa de su ruina.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Mas el que me escucha, habitará seguro, y vivirá tranquilo sin temer el mal.

< Karin Magana 1 >