< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Provérbios de Salomão, filho de Davi, rei de Israel.
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
Para conhecer a sabedoria e a instrução; para entender as palavras da prudência;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
Para obter a instrução do entendimento; justiça, juízo e equidades;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
Para dar inteligência aos simples, conhecimento e bom senso aos jovens.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
O sábio ouvirá, e crescerá em conhecimento; o bom entendedor obterá sábios conselhos.
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
Para entender provérbios e [sua] interpretação; as palavras dos sábios, e seus enigmas.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
O temor ao SENHOR [é] o principio do conhecimento; os tolos desprezam a sabedoria e a instrução.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Filho meu, ouve a instrução de teu pai; e não abandones a doutrina de tua mãe.
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
Porque [serão] um ornamento gracioso para tua cabeça; e colares para teu pescoço.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Filho meu, se os pecadores tentarem te convencer, não te deixes influenciar.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Se disserem: Vem conosco, vamos espiar [derramamento] de sangue; preparemos uma emboscada ao inocente sem razão.
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Vamos tragá-los vivos, como o Xeol; e inteiros, como os que descem à cova. (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Acharemos toda espécie de coisas valiosas, encheremos nossas casas de despojos.
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Lança tua sorte entre nós, compartilharemos todos de uma [só] bolsa.
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Filho meu, não sigas teu caminho com eles; desvia teu pé [para longe] de onde eles passarem;
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
Porque os pés deles correm para o mal, e se apressam para derramar sangue.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Certamente [é] inútil se estender a rede diante da vista de todas as aves;
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Porém estes estão esperando [o derramamento] de seu [próprio] sangue; e preparam emboscada para suas [próprias] almas.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Assim [são] os caminhos de todo aquele que tem ganância pelo lucro desonesto; ela tomará a alma daqueles que a tem.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
A sabedoria grita pelas ruas; nas praças ela levanta sua voz.
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
Ela clama nas encruzilhadas, onde [passam] muita gente; às entradas das portas, nas cidades ela diz suas mensagens:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Até quando, ó tolos, amareis a tolice? E vós zombadores, desejareis a zombaria? E [vós] loucos, odiareis o conhecimento?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Convertei-vos à minha repreensão; eis que vos derramarei meu espírito, [e] vos farei saber minhas palavras.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
[Mas] porque eu clamei, e recusastes; estendi minha mão, e não houve quem desse atenção,
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
E rejeitastes todo o meu conselho, e não quisestes minha repreensão,
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
Também eu rirei em vosso sofrimento, [e] zombarei, quando vier vosso medo.
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
Quando vier vosso temor como tempestade, e a causa de vosso sofrimento como ventania, quando vier sobre vós a opressão e a angústia,
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Então clamarão a mim; porém eu não responderei; de madrugada me buscarão, porém não me acharão.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Porque odiaram o conhecimento; e escolheram não temer ao SENHOR.
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Não concordaram com meu conselho, [e] desprezaram toda a minha repreensão.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Por isso comerão do fruto do seu [próprio] caminho, e se fartarão de seus [próprios] conselhos.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Pois o desvio dos tolos os matará, e a confiança dos loucos os destruirá.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Porém aquele que me ouvir habitará em segurança, e estará tranquilo do temor do mal.

< Karin Magana 1 >