< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Proverbes de Salomon, fils de David, roi d’Israël,
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
pour connaître la sagesse et l’instruction, pour discerner les paroles d’intelligence;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
pour recevoir instruction dans la sagesse, la justice, le juste jugement, et la droiture;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
pour donner aux simples de la prudence, au jeune homme de la connaissance et de la réflexion.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Le sage écoutera, et croîtra en science, et l’intelligent acquerra du sens
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
pour comprendre un proverbe et une allégorie, les paroles des sages et leurs énigmes.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
La crainte de l’Éternel est le commencement de la connaissance; les fous méprisent la sagesse et l’instruction.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Écoute, mon fils, l’instruction de ton père, et n’abandonne pas l’enseignement de ta mère;
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
car ce sera une guirlande de grâce à ta tête, et des colliers à ton cou.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Mon fils, si les pécheurs cherchent à te séduire, n’y acquiesce pas.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
S’ils disent: Viens avec nous, nous serons aux embûches pour le sang, nous nous cacherons pour [guetter] l’innocent, sans cause;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
nous les engloutirons vivants, comme le shéol, et tout entiers comme ceux qui descendent dans la fosse; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
nous trouverons toute sorte de biens précieux, nous remplirons nos maisons de butin;
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
prends ton lot parmi nous, il n’y aura qu’une bourse pour nous tous:
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
mon fils, ne fais pas route avec eux, retiens ton pied de leur sentier;
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
car leurs pieds courent au mal, et ils se hâtent pour verser le sang.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Car en vain le filet est étendu devant les yeux de tout ce qui a des ailes;
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
et eux, ils sont aux embûches contre leur propre sang, ils se cachent pour [guetter] leurs propres âmes.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Telles sont les voies de tout homme qui cherche le gain déshonnête, lequel ôte la vie à ceux qui le possèdent.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
La sagesse crie au-dehors, elle fait retentir sa voix sur les places;
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
elle crie à l’entrée des lieux bruyants, aux ouvertures des portes; elle prononce ses paroles dans la ville:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Simples, jusques à quand aimerez-vous la simplicité, et [jusques à quand] les moqueurs prendront-ils plaisir à la moquerie, et les sots haïront-ils la connaissance?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Revenez à ma répréhension; voici, je ferai couler pour vous mon esprit, je vous ferai savoir mes paroles.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Parce que j’ai crié et que vous avez refusé [d’écouter], parce que j’ai étendu ma main et que personne n’a pris garde,
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
et que vous avez rejeté tout mon conseil et que vous n’avez pas voulu de ma répréhension,
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
moi aussi je rirai lors de votre calamité, je me moquerai quand viendra votre frayeur,
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
quand votre frayeur viendra comme une subite destruction et que votre calamité arrivera comme un tourbillon, quand la détresse et l’angoisse viendront sur vous:
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
alors ils crieront vers moi, et je ne répondrai pas; ils me chercheront de bonne heure, mais ils ne me trouveront point.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Parce qu’ils ont haï la connaissance et qu’ils n’ont pas choisi la crainte de l’Éternel,
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
qu’ils n’ont point voulu de mon conseil, qu’ils ont méprisé toute ma répréhension,
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
ils mangeront du fruit de leur voie et seront rassasiés de leurs propres conseils.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Car la révolte des simples les tue, et la prospérité des sots les fait périr.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Mais celui qui m’écoute habitera en sécurité et sera tranquille, sans crainte du mal.

< Karin Magana 1 >