< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
The proverbs of Solomon, the son of David, king of Israel:
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
That one may learn wisdom and instruction, And receive words of understanding;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
That one may gain the instruction of prudence, Justice, equity, and uprightness;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
Which will give caution to the simple, To the young man wisdom and discretion;
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Let the wise man hear, and he will increase his knowledge, And the man of understanding will gain wise counsels;
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
So as to understand a proverb and a deep maxim, The words of the wise and their dark sayings.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
The fear of the LORD is the beginning of knowledge; Fools despise wisdom and instruction.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Hear, O my son! the instruction of thy father, And neglect not the teaching of thy mother!
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
For they shall be a graceful wreath for thy head, And a chain around thy neck.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
My son, if sinners entice thee, Consent thou not!
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
If they say, “Come with us, Let us lie in wait for blood, Let us lurk secretly for him who is innocent in vain;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Let us swallow them up alive, like the underworld, Yea, in full health, as those that go down into the pit; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
We shall find all kinds of precious substance, We shall fill our houses with spoil;
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Thou shalt cast thy lot among us; We will all have one purse;”—
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
My son, walk thou not in their way, Refrain thy foot from their path!
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
For their feet run to evil, And make haste to shed blood.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
For as the net is spread in vain Before the eyes of any bird,
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
So they lie in wait for their own blood; They lurk secretly for their own lives.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Such are the ways of every one greedy of unjust gain; It taketh away the life of the possessor thereof.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Wisdom crieth out in the highway; In the market-place she uttereth her voice;
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
At the head of the noisy streets she crieth aloud; At the entrances of the gates, throughout the city, she proclaimeth her words [[saying]]:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
How long, ye simple ones, will ye love simplicity? How long will scoffers delight themselves in scoffing, And fools hate knowledge?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Turn ye at my reproof! Behold, I will pour out my spirit to you; I will make known my words to you!
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
“Because I have called, and ye have refused, —Because I have stretched out my hand, and no one hath regarded.
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
Because ye have rejected all my counsel, And have slighted my rebuke, —
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
I also will laugh at your calamity, I will mock when your fear cometh;
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
When your fear cometh upon you like a storm. And destruction overtaketh you like a whirlwind, When distress and anguish come upon you.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Then will they call upon me, but I will not answer! They will seek me early, But they shall not find me!
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Because they have hated knowledge, And have not chosen the fear of the LORD, —
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Because they would not attend to my counsel, And have despised all my reproof, —
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Therefore shall they eat of the fruit of their own way, And be filled to the full with their own devices;
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Yea, the turning away of the simple shall slay them, And the carelessness of fools shall destroy them.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
But whoso hearkeneth to me shall dwell securely, And shall not be disquieted with the fear of evil.”

< Karin Magana 1 >