< Filibbiyawa 1 >

1 Bulus da Timoti, bayin Kiristi Yesu, Zuwa ga dukan tsarkaka cikin Kiristi Yesu a Filibbi, tare da masu kula da Ikkilisiya da kuma masu hidima.
Paulus og Timotheus, Kristi Jesu Tjenere, til alle de hellige i Kristus Jesus, som ere i Filippi, med Tilsynsmænd og Menighedstjenere.
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare ku.
Naade være med eder og Fred fra Gud vor Fader og den Herre Jesus Kristus!
3 Ina gode wa Allahna a kowane lokacin da na tuna da ku.
Jeg takker min Gud, saa ofte jeg kommer eder i Hu,
4 A cikin dukan addu’o’ina dominku duka, nakan yi addu’a da farin ciki kullum
idet jeg altid, i hver min Bøn, beder for eder alle med Glæde,
5 saboda tarayyarku a cikin bishara daga ranar farko har yă zuwa yanzu,
for eders Deltagelse i Evangeliet fra den første Dag indtil nu;
6 da tabbacin cewa wanda ya fara kyakkyawan aikin nan a cikinku, zai kai shi ga kammalawa har yă zuwa ranar Kiristi Yesu.
forvisset om dette, at han, som begyndte en god Gerning i eder, vil fuldføre den indtil Jesu Kristi Dag,
7 Daidai ne in yi wannan tunani game da dukanku, da yake kuna a zuciyata; domin ko ina daure cikin sarƙoƙi ko ina kāre bishara ina kuma tabbatar da ita, dukanku kuna tarayya cikin alherin Allah tare da ni.
saaledes som det jo er ret for mig at mene dette om eder alle, efterdi jeg har eder i Hjertet baade under mine Lænker og under Evangeliets Forsvar og Stadfæstelse, fælles som I jo alle ere med mig om Naaden.
8 Allah shi ne shaidata, ya san yadda nake ƙaunarku duka da ƙaunar Kiristi Yesu.
Thi Gud er mit Vidne, hvorledes jeg længes efter eder alle med Kristi Jesu inderlige Kærlighed.
9 Addu’ata ita ce ƙaunarku tă yi ta cin gaba da ƙaruwa cikin sani da kuma zurfin ganewa,
Og derom beder jeg, at eders Kærlighed fremdeles maa blive mere og mere rig paa Erkendelse og al Skønsomhed,
10 don ku iya rarrabe abin da yake mafi kyau, ku kuma zama da tsarki, marasa aibi har yă zuwa ranar Kiristi,
saa I kunne værdsætte de forskellige Ting, for at I maa være rene og uden Anstød til Kristi Dag,
11 cikakku da sakamakon aikin adalci da yake zuwa ta wurin Yesu Kiristi, zuwa ga ɗaukakar Allah da kuma yabonsa.
fyldte med Retfærdigheds Frugt, som virkes ved Jesus Kristus, Gud til Ære og Pris.
12 To, ina so ku sani’yan’uwa, cewa abin da ya faru da ni ya sa cin gaban bishara.
Men jeg vil, I skulle vide, Brødre! at mine Forhold snarere have tjent til Evangeliets Fremme,
13 Ta haka, ya zama sananne ga dukan masu gadin fada da kuma ga kowa cewa an daure ni da sarƙoƙi saboda Kiristi.
saa at det er blevet aabenbart for hele Livvagten og for alle de øvrige, at mine Lænker bæres for Kristi Skyld,
14 Saboda sarƙoƙina, yawancin’yan’uwa cikin Ubangiji sun sami ƙarfafawa su yi maganar Allah gabagadi da kuma babu tsoro.
og de fleste af Brødrene fik i Tillid til Herren ved mine Lænker end mere Dristighed til at tale Guds Ord uden Frygt.
15 Gaskiya ce cewa waɗansu suna yin wa’azin Kiristi saboda kishi da neman faɗa, amma waɗansu da nufi mai kyau suke yi.
Nogle prædike vel ogsaa Kristus for Avinds og Kivs Skyld, men nogle ogsaa i en god Mening.
16 Na biye suna yin haka cikin ƙauna, da sanin cewa an sa ni a nan ne domin kāriyar bishara.
Disse gøre det af Kærlighed, vidende, at jeg er sat til at forsvare Evangeliet;
17 Na farin dai suna wa’azin Kiristi da sonkai ne, ba da zuciya ɗaya ba, a sonsu, su wahalar da ni a cikin sarƙoƙi.
men hine forkynde Kristus af Egennytte, ikke ærligt, men i den Tanke at føje Trængsel til mine Lænker.
18 Me kuma? Ta ko yaya dai, ko da gangan, ko da gaske, ana shelar Kiristi. Domin wannan kuwa ina farin ciki. I, zan kuwa ci gaba da farin ciki,
Hvad saa? Kristus forkyndes dog paa enhver Maade, være sig paa Skrømt eller i Sandhed; og derover glæder jeg mig, og jeg vil ogsaa fremdeles glæde mig.
19 gama na san cewa ta wurin addu’o’inku da kuma taimako daga Ruhun Yesu Kiristi, abin da ya same ni zai zama sanadin kuɓutata.
Thi jeg ved, at dette skal blive mig til Frelse ved eders Bøn og Jesu Kristi Aands Hjælp,
20 Ina saurara da marmari da kuma bege cewa ba zan taɓa shan kunya ba, sai dai zan sami issashen ƙarfin hali yanzu kamar kullum, za a ɗaukaka Kiristi a jikina, ko ta wurin rayuwa ko kuma ta wurin mutuwa.
efter min Længsel og mit Haab, at jeg i intet skal blive til Skamme, men at Kristus skal med al Frimodighed, som altid, saa ogsaa nu, forherliges i mit Legeme, være sig ved Liv eller ved Død.
21 Gama a gare ni, rai Kiristi ne, mutuwa kuma riba ce.
Thi det at leve er mig Kristus og at dø en Vinding.
22 In zan ci gaba da rayuwa a cikin jiki, wannan zai zama aiki mai amfani a gare ni. Duk da haka me zan zaɓa? Ban sani ba!
Men dersom dette at leve i Kødet skaffer mig Frugt af min Gerning, saa ved jeg ikke, hvad jeg skal vælge;
23 Na rasa wanda zan zaɓa cikin biyun nan. Ina sha’awa in yi ƙaura in zauna tare da Kiristi, wannan kuwa ya fi kyau nesa ba kusa ba;
men jeg staar tvivlraadig imellem de to Ting, idet jeg har Lysten til at bryde op og være sammen med Kristus; thi dette var saare meget bedre;
24 amma ya fi muku muhimmanci in rayu cikin jiki.
men at forblive i Kødet er mere nødvendigt for eders Skyld.
25 Na tabbata haka ne, na kuwa san zan wanzu in zauna tare da ku duka, domin ku ci gaba, bangaskiyarku tana sa ku farin ciki,
Og i Forvisning herom ved jeg, at jeg skal blive i Live og forblive hos eder alle til eders Fremgang og Glæde i Troen,
26 domin ta wurin kasancewata tare da ku, farin cikinku cikin Kiristi Yesu zai cika sosai ta dalilina.
for at eders Ros ved mig kan blive rig i Kristus Jesus, ved at jeg atter kommer til Stede iblandt eder.
27 Kome ya faru, ku yi zaman da ya cancanci bisharar Kiristi. Ta haka, ko na zo na gan ku, ko ban zo ba, in ji labari cewa kun tsaya da ƙarfi a cikin ruhu ɗaya, kuna fama kamar mutum ɗaya saboda bangaskiyar bishara
Kun skulle I leve Kristi Evangelium værdigt, for at, hvad enten jeg kommer og ser eder eller er fraværende, jeg dog kan høre om eder, at I staa faste i een Aand, saa at I med een Sjæl stride tilsammen for Troen paa Evangeliet
28 ba tare da kun ji tsoron waɗanda suke gāba da ku ta kowace hanya ba. Wannan alama ce a gare su cewa za a hallaka su, amma a gare ku za a cece ku, wannan tabbacin kuwa daga wurin Allah ne.
og ikke lade eder forfærde i nogen Ting af Modstanderne; thi dette er for dem et Tegn paa Undergang, men for eder paa Frelse, og det fra Gud.
29 Gama an ba ku zarafi a madadin Kiristi cewa ba gaskatawa da shi kaɗai ba kuka yi ba, har ma ku sha wahala dominsa,
Thi eder er det forundt for Kristi Skyld — ikke alene at tro paa ham, men ogsaa at lide for hans Skyld,
30 da yake kuna shan faman da kuka gan na sha, kuna kuma jin cewa har yanzu ina sha.
idet I have den samme Kamp, som I have set paa mig og nu høre om mig.

< Filibbiyawa 1 >