< Obadiya 1 >

1 Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
Видіння Овді́я. Так сказав Господь Бог на Едо́м: „Почули ми вістку від Господа, і по́сланий був між наро́дів посо́л, щоб сказати: Уставайте, і станьмо на нього до бо́ю!
2 “Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
Оце Я мали́м тебе дав між наро́ди, ти дуже пого́рджений.
3 Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
Гордість серця твого обманила тебе, який перебува́єш по щі́линах ске́льних, у високім сиді́нні своїм, що гово́риш у серці своє́му: Хто скине на землю мене́?
4 Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
Якщо б ти підні́сся, немов той орел, і якщо б ти кубло́ своє склав поміж зо́рями, — то й звідти Я скину тебе, промовляє Госпо́дь!
5 “In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
Чи ж до тебе злоді́ї прихо́дили, чи нічні ті грабі́жники, — такий ти пони́щений! — чи ж вони не накра́ли б собі скільки треба? Якщо б до тебе прийшли збирачі́ винограду, чи ж вони не лишили б хоч ви́бірків?
6 Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
Як Ісав перешу́каний, як криї́вки його перегля́нені!
7 Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
Аж до границі прогнали тебе, обма́нять тебе твої всі сою́зники, переможуть тебе твої при́ятелі! Ті, що хліб твій їдять, пастку розста́влять на тебе, — нема в тому розуму!
8 “A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
Чи ж не станеться це того дня, — промовляє Господь, — і ви́гублю Я мудреці́в із Едо́му, а розум з гори Ісавової?
9 Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
І настра́шене буде лица́рство твоє, о Тема́не, щоб був ви́тятий кожен з Ісава уби́вством.
10 Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
Через насилля на Якова на брата твого сором покриє тебе, і ти ви́тятий будеш наві́ки.
11 A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
Того дня, коли став ти навпро́ти, того дня, як чужі полони́ли були його ві́йсько, і коли чужинці́ в його брами ввійшли і же́реба кидали про Єрусалим, то й ти був, як один з них!
12 Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
І тому́ не дивися на день свого брата, на день лиха його, і не тішся з Юдиних синів у день їхньої згу́би, і не розкривай своїх уст у день у́тиску.
13 Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
І не входь ти до брами наро́ду Мого́ у день лиха його́, і не пригляда́йся до зла його й ти в день нещастя його́, і не простяга́йте своєї руки́ до багатства його́ в день нещастя його́!
14 Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
І на роздорі́жжі не стій, щоб витина́ти його втікачі́в, і в день у́тиску не видавай його ре́шток!
15 “Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
Бо близьки́й день Госпо́дній над усіма наро́дами, — як зробив ти, то так і тобі буде зро́блено: ве́рнеться на твою го́лову чин твій!
16 Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
Бо я́к ви пили́ на святій Моїй горі, так народи усі за́вжди пи́тимуть! І будуть пити вони, і бу́дуть хлепта́ти, і стануть вони, немов їх не було́.
17 Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
А на Сіонській горі буде спасі́ння, і буде святою вона, і спа́дки свої́ вже пося́де дім Яковів.
18 Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
І дім Якова стане огнем, і дім Йо́сипа — по́лум'ям, а дім Ісава — соломою, — і будуть пала́ти вони проти них, і їх пожеру́ть, і останку не буде із дому Ісава, бо Госпо́дь це сказав.
19 Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
І пося́дуть півде́нні Іса́вову го́ру, а мешка́нці долин — филисти́млян, і пося́дуть Єфремове поле та поле самарі́йське, а Веніями́н — Ґілеа́д.
20 Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
А полоне́ні ві́йська Ізраїлевих синів заволодіють тим, що хананейське аж до Цорфа́ту, а єрусалимські вигнанці в неволі, що в Сефараді, пося́дуть міста́ полудне́ві.
21 Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.
І спаси́телі при́йдуть на го́ру Сіо́н, щоб го́ру Іса́ва судити, — і царство Господнє настане!

< Obadiya 1 >