< Obadiya 1 >

1 Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
رویای عوبدیا.۱
2 “Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
هان من تو راکوچکترین امت‌ها گردانیدم و تو بسیار خوارهستی.۲
3 Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
‌ای که در شکافهای صخره ساکن هستی و مسکن تو بلند می‌باشد و در دل خود می‌گویی کیست که مرا به زمین فرود بیاورد، تکبر دلت، تورا فریب داده است.۳
4 Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
خداوند می‌گوید: اگرچه خویشتن را مثل عقاب بلند سازی و آشیانه خودرا در میان ستارگان بگذاری من تو را از آنجا فرودخواهم آورد.۴
5 “In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
اگر دزدان یا غارت کنندگان شب نزد تو آیند، (چگونه هلاک شدی )؟ آیا بقدرکفایت غارت نمی کنند؟ و اگر انگورچینان نزد توآیند آیا بعضی خوشه‌ها را نمی گذارند؟۵
6 Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
چیزهای عیسو چگونه تفتیش شده و چیزهای مخفی او چگونه تفحص گردیده است؟۶
7 Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
همه آنانی که با تو همعهد بودند تو را بسرحدفرستادند و صلح اندیشان تو، تو را فریب داده، برتو غالب آمدند و خورندگان نان تو دامی زیر توگستردند. در ایشان فطانتی نیست.۷
8 “A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
خداوند می‌گوید: آیا در آن روز حکیمان ادوم را و فطانت را از کوه عیسو نابود نخواهم گردانید؟۸
9 Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
و جباران تو‌ای تیمان هراسان خواهندشد تا هر کس از کوه عیسو به قتل منقطع شود.۹
10 Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
به‌سبب ظلمی که بر برادرت یعقوب نمودی، خجالت تو را خواهد پوشانید و تا به ابد منقطع خواهی شد.۱۰
11 A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
در روزی که به مقابل وی ایستاده بودی، هنگامی که غریبان اموال او را غارت نمودند وبیگانگان به دروازه هایش داخل شدند و براورشلیم قرعه انداختند، تو نیز مثل یکی از آنهابودی.۱۱
12 Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
بر روز برادر خود هنگام مصیبتش نگاه مکن و بر بنی یهودا در روز هلاکت ایشان شادی منما و در روز تنگی ایشان لاف مزن.۱۲
13 Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
و به دروازه های قوم من در روز بلای ایشان داخل مشو و تو نیز بر بدی ایشان در روز بلای ایشان منگر و دست خود را بر اموال ایشان در روز بلای ایشان دراز مکن.۱۳
14 Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
و بر سر دو راه مایست تافراریان ایشان را منقطع سازی و باقی ماندگان ایشان را در روز تنگی تسلیم منما.۱۴
15 “Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
زیرا که روزخداوند بر جمیع امت‌ها نزدیک است و چنانکه عمل نمودی همچنان به تو عمل کرده خواهدشد و اعمالت بر سرت خواهد برگشت.۱۵
16 Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
زیراچنانکه بر کوه مقدس من نوشیدید، همچنان جمیع امت‌ها خواهند نوشید و آشامیده، خواهندبلعید و چنان خواهند شد که گویا نبوده‌اند.۱۶
17 Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
اما بر کوه صهیون نجات خواهد بود ومقدس خواهد شد و خاندان یعقوب میراث خودرا به تصرف خواهند‌آورد.۱۷
18 Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
و خاندان یعقوب آتش و خاندان یوسف شعله و خاندان عیسو کاه عوبدیا خواهند بود و در میان ایشان مشتعل شده، ایشان را خواهد سوزانید و برای خاندان عیسو بقیتی نخواهد ماند زیرا خداوند تکلم نموده است.۱۸
19 Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
واهل جنوب کوه عیسو را و اهل هامون فلسطینیان را به تصرف خواهند‌آورد و صحرای افرایم وصحرای سامره را به تصرف خواهند‌آورد وبنیامین جلعاد را (متصرف خواهد شد).۱۹
20 Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
و اسیران این لشکر بنی‌اسرائیل ملک کنعانیان راتا صرفه به تصرف خواهند‌آورد و اسیران اورشلیم که در صفارد هستند شهرهای جنوب را به تصرف خواهند‌آورد.۲۰
21 Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.
و نجات دهندگان به کوه صهیون برآمده، بر کوه عیسو داوری خواهند کرد و ملکوت از آن خداوند خواهدشد.۲۱

< Obadiya 1 >