< Obadiya 1 >

1 Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
Obadias' syn. Så sier Herren, Israels Gud, om Edom: En tidende har vi hørt fra Herren, og et bud er sendt ut blandt hedningefolkene: Stå op og la oss reise oss til strid mot det!
2 “Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
Se, liten vil jeg gjøre dig blandt hedningefolkene; du skal bli dypt foraktet.
3 Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
Ditt hjertes overmot har dåret dig, du som bor i fjellkløfter, i din høie bolig, du som sier i ditt hjerte: Hvem vil styrte mig ned til jorden?
4 Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
Om du bygger høit som ørnen og setter ditt rede blandt stjerner, vil jeg styrte dig ned derfra, sier Herren.
5 “In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
Om tyver kom til dig eller røvere om natten - å, hvor du blir tilintetgjort! - mon de da vilde stjele mere enn det de trengte? Om det kom til dig folk som vilde høste din vin, vilde de da ikke levne en efterhøst?
6 Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
Men hvor blir ikke Esau ransaket, og hans skjulte skatter opsøkt!
7 Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
Like til grensen følger alle dine forbundsfeller dig; dine gode venner sviker dig og får overhånd over dig; de menn som eter ditt brød, legger en snare for dig. Det er ingen forstand hos ham!
8 “A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
Skal jeg ikke på den dag, sier Herren, gjøre ende på alle vismenn i Edom og all forstand på Esaus berg?
9 Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
Dine kjemper, Teman, skal bli motløse, så hver mann blir drept og utryddet på Esaus berg.
10 Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
For den vold du har gjort mot din bror Jakob, skal skam dekke dig, og du skal bli utryddet til evig tid.
11 A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
Den dag da du holdt dig unda, den dag da fremmede bortførte hans gods, og utlendinger gikk inn i hans porter og kastet lodd om Jerusalem, da var også du som en av dem.
12 Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
Se ikke med skadefryd på din brors dag, på hans ulykkes dag, og gled dig ikke over Judas barn på deres undergangs dag, og lukk ikke din munn så vidt op på trengselens dag!
13 Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
Dra ikke inn gjennem mitt folks port den dag de er i nød, se ikke også du med skadefryd på deres ulykke den dag de er i nød, og legg ikke hånd på deres gods den dag de er i nød,
14 Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
og stå ikke på veiskjellet for å utrydde dem av mitt folk som har sloppet unda, og overgi ikke dets flyktninger til fienden på trengselens dag!
15 “Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
For nær er Herrens dag over alle folkene; som du har gjort, skal det gjøres med dig, dine gjerninger skal falle tilbake på ditt eget hode.
16 Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
For likesom I har drukket på mitt hellige berg, skal alle folkene drikke uten å holde op; de skal drikke i fulle drag og bli som om de aldri hadde vært til.
17 Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
Men på Sions berg skal det være en flokk av undslopne, og det skal være hellig; og Jakobs hus skal ta sine eiendommer i eie.
18 Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
Og Jakobs hus skal bli en ild, og Josefs hus en lue, og Esaus hus skal bli til halm, og de skal sette ild på det og fortære det, og det skal ikke bli nogen tilbake av Esaus hus, for Herren har talt.
19 Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
Og de som bor i sydlandet, skal ta Esaus berg i eie, og de som bor i lavlandet, skal ta filistrenes land, og de skal ta Efra'ims land og Samarias land i eie, og Benjamin skal ta Gilead,
20 Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
og de av denne Israels hær som er bortført, skal ta det som finnes av kana'anitter like til Sarepta, og de bortførte fra Jerusalem som er i Sefarad, skal ta sydlandets byer i eie.
21 Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.
Og frelsere skal dra op på Sions berg og dømme Esaus berg, og riket skal høre Herren til.

< Obadiya 1 >