< Obadiya 1 >

1 Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
Vision d’Abdias. Voici ce que dit le Seigneur Dieu à Edom: [Nous avons entendu une nouvelle venant du Seigneur; et il a envoyé un messager vers les nations: Levez-vous, et levons-nous ensemble contre lui pour le combat].
2 “Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
Voici que je t’ai placé très petit parmi les nations, tu es fort méprisable.
3 Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
L’orgueil de ton cœur t’a élevé, toi habitant dans les fentes des rochers, exaltant ton trône; toi qui dis dans ton cœur: Qui me fera descendre à terre?
4 Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
Si tu t’élèves comme l’aigle, et que parmi les astres tu poses ton nid, je t’en ferai descendre, dit le Seigneur.
5 “In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
Si des voleurs, si des brigands étaient entrés chez toi durant la nuit, comment aurais-tu gardé le silence? N’auraient-ils pas volé ce qui leur suffisait? Si des vendangeurs étaient entrés chez toi, est-ce qu’ils ne t’auraient pas laissé au moins une grappe de raisin?
6 Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
Comment les ennemis ont-ils fouillé Esaü, fureté dans ce qu’il avait de caché?
7 Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
Ils t’ont éconduit jusqu’à la frontière; tous tes alliés se sont joués de toi; les hommes qui vivaient en paix avec toi ont prévalu contre toi; ceux qui mangent ton pain dresseront des embûches sous tes pas; il n’y a pas de prudence en lui.
8 “A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
N’est-ce pas en ce jour-là, dit le Seigneur, que je perdrai les sages de l’Idumée et bannirai la prudence de la montagne d’Esaü?
9 Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
Et ils craindront, tes braves du midi, que l’homme de la montagne d’Esaü ne périsse.
10 Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
À cause de tes meurtres et à cause de ton iniquité contre Jacob ton frère, la confusion te couvrira, et tu périras pour jamais.
11 A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
Au jour que tu t’élevais contre lui, quand des ennemis se rendaient maîtres de son armée, et que des étrangers entraient dans ses portes, et que sur Jérusalem ils jetaient le sort, toi aussi tu étais comme l’un d’entre eux.
12 Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
Et tu ne mépriseras pas ton frère en son jour malheureux, au jour de son exil, et tu ne te réjouiras pas sur les fils de Juda au jour de leur ruine; et tu ne parleras pas orgueilleusement au jour de l’angoisse.
13 Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
Et tu n’entreras pas dans la porte de mon peuple au jour de leur ruine; et tu ne les mépriseras pas, toi non plus, au milieu de ses maux, au jour de sa désolation; et tu ne seras pas envoyé contre son armée au jour de sa désolation.
14 Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
Et tu ne te tiendras pas dans les carrefours, afin de tuer ceux qui fuiront, et tu n’enfermeras pas les restes de ses habitants au jour de la tribulation.
15 “Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
Parce que le jour du Seigneur est près d’éclater sur toutes les nations; comme tu as fait, il te sera fait; ce que tu leur as fait, il le fera retomber sur ta tête.
16 Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
Car comme vous avez bu sur ma montagne sainte, toutes les nations boiront sans discontinuer; et elles boiront, elles avaleront, et elles seront comme si elles n’étaient point.
17 Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
Mais sur la montagne de Sion sera le salut et elle sera sainte: la maison de Jacob possédera ceux qui l’avaient possédée.
18 Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
Et la maison de Jacob sera un feu, et la maison de Joseph une flamme, et la maison d’Esaü une paille; et ils l’embraseront, et ils la dévoreront, et il n’y aura pas de restes de la maison d’Esaü, parce que le Seigneur a parlé.
19 Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
Et ceux qui sont au midi hériteront de la montagne d’Esaü; et ceux qui sont dans les plaines assujettiront les Philistins; et ils posséderont la contrée d’Ephraïm et la contrée de Samarie, et Benjamin possédera Galaad.
20 Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
Et les exilés de cette armée des enfants d’Israël posséderont tous les lieux des Chananéens jusqu’à Sarepta; et les exilés de Jérusalem, qui sont sur le Bosphore, posséderont les cités du midi.
21 Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.
Et les libérateurs monteront sur la montagne de Sion pour juger la montagne d’Esaü; et le règne sera au Seigneur.

< Obadiya 1 >