< Obadiya 1 >
1 Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
The vision of 'Obadiah: Thus hath said the Lord Eternal concerning Edom, A rumor have we heard from the Lord, and an ambassador is sent among the nations, Arise ye, and let us rise up against her to war.
2 “Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
Behold, I make thee small among the nations: thou shalt be greatly despised.
3 Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
The presumption of thy heart hath beguiled thee, thou that dwellest in the clefts of the rock, whose habitation is high; that saith in his heart, Who shall bring me down to the ground?
4 Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
Though thou wert to rise as high as the eagle, and though thou set thy nest among the stars, thence will I bring thee down, saith the Lord.
5 “In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
How? are thieves come to thee? or night-prowling robbers? how destroyed art thou! would they not have stolen till they had enough? if grape-gatherers had come to thee, would they not have left some gleanings?
6 Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
How are [the treasures] of Esau searched out! how are his hidden things laid open!
7 Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
Up to the border have accompanied thee all the men of thy confederacy; beguiled, overcome thee have the men that were at peace with thee: [they that eat] thy bread have struck thee secretly a wound. There is no understanding in him.
8 “A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
Shall I not on that same day, saith the Lord, even destroy the wise men out of Edom, and understanding out of the mount of Esau?
9 Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
And thy mighty men, O Theman, shall be dismayed, in order that every one from the mount of Esau may be cut off by slaughter.
10 Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
Because of thy violence against thy brother Jacob shall shame cover thee, and thou shalt be cut off for ever.
11 A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
On the day that thou stoodest on the other side, on the day that strangers carried away captive his army, and foreigners entered into his gates, and cast lots over Jerusalem, also thou wast as any one of them.
12 Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
But thou shouldst not have looked on [pleased] at the day of thy brother, on the day that he was delivered up to strangers; neither shouldst thou have rejoiced over the children of Judah on the day of their destruction; nor should thou have spoken proudly on the day of distress.
13 Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
Thou shouldst not have entered into the gate of my people on the day of their calamity; yea, thou too shouldst not have looked [pleased] on their affliction on the day of their calamity; nor have laid hands on their army on the day of their calamity;
14 Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
Neither shouldst thou have stood in the crossway, to cut off those of his that did escape; neither shouldst thou have delivered up those of his that did remain on the day of distress.
15 “Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
For near is the day of the Lord over all the nations: as thou hast done, shall it be done unto thee; thy deeds shall return upon thy own head.
16 Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
For as ye have drunk upon my holy mount, so shall all the nations drink continually; yea, they shall drink, and they shall reel about, and they shall be as though they had not been.
17 Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
But upon mount Zion shall be deliverance, and it shall be holy: and the house of Jacob shall again possess their inheritances.
18 Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
And the house of Jacob shall be a fire, and the house of Joseph a flame, and the house of Esau become stubble, and they shall set them on fire, and devour them; and there shall not be any one remaining of the house of Esau; for the Lord hath spoken it.
19 Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
And they of the south shall possess the mount of Esau; and they of the lowlands, the Philistines; and they shall possess the fields of Ephraim, and the fields of Samaria: and Benjamin [shall possess] Gil'ad.
20 Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
And the exiles of this host of the children of Israel that are [with] the Canaanites, as far as Zarephath, and the exiles of Jerusalem, who are in Sepharad, shall possess the cities of the south.
21 Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.
And deliverers shall go up on mount Zion to judge the mount of Esau: and the kingdom shall be the Lord's