< Obadiya 1 >

1 Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
The vision of Obadiah. Thus saith the Lord God against Edom, We haue heard a rumour from the Lord, and an ambassadour is sent among the heathen: arise, and let vs rise vp against her to battel.
2 “Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
Beholde, I haue made thee small among the heathen: thou art vtterly despised.
3 Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
The pride of thine heart hath deceiued thee: thou that dwellest in the cleftes of the rockes, whose habitation is hie, that saith in his heart, Who shall bring me downe to the ground?
4 Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
Though thou exalt thy selfe as the eagle, and make thy nest among the starres, thence will I bring thee downe, sayth the Lord.
5 “In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
Came theeues to thee or robbers by night? howe wast thou brought to silence? woulde they not haue stolen, til they had ynough? if the grape gatherers came to thee, woulde they not leaue some grapes?
6 Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
Howe are the things of Esau sought vp, and his treasures searched?
7 Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
All the men of thy confederacie haue driuen thee to ye borders: the men that were at peace with thee, haue deceiued thee, and preuailed against thee: they that eate thy bread, haue laid a wound vnder thee: there is none vnderstanding in him.
8 “A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
Shall not I in that day, saith the Lord, euen destroy the wise men out of Edom, and vnderstanding from the mount of Esau?
9 Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
And thy strong men, O Teman, shall bee afraide, because euery one of the mount of Esau shalbe cut off by slaughter.
10 Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
For thy crueltie against thy brother Iaakob, shame shall couer thee, and thou shalt be cut off for euer.
11 A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
When thou stoodest on the other side, in the day that the strangers caried away his substance, and straungers entred into his gates, and cast lots vpon Ierusalem, euen thou wast as one of them.
12 Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
But thou shouldest not haue beholden the day of thy brother, in the day that hee was made a stranger, neither shouldest thou haue reioyced ouer the children of Iudah, in the day of their destruction: thou shouldest not haue spoken proudly in the day of affliction.
13 Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
Thou shouldest not haue entred into the gate of my people, in the day of their destruction, neither shouldest thou haue once looked on their affliction in the day of their destruction, nor haue layde hands on their substance in the day of their destruction.
14 Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
Neyther shouldest thou haue stande in the crosse wayes to cut off them, that shoulde escape, neither shouldest thou haue shut vp the remnant thereof in the day of affliction.
15 “Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
For the day of the Lord is neere, vpon all the heathen: as thou hast done, it shall bee done to thee: thy reward shall returne vpon thine head.
16 Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
For as yee haue drunke vpon mine holy Mountaine, so shall all the heathen drinke continually: yea, they shall drinke and swallow vp, and they shalbe as though they had not bene.
17 Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
But vpon mount Zion shalbe deliuerance, and it shalbe holy, and the house of Iaakob shall possesse their possessions,
18 Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
And the house of Iaakob shalbe a fire, and the house of Ioseph a flame, and the house of Esau as stubble, and they shall kindle in them and deuoure them: and there shall bee no remnant of the house of Esau for the Lord hath spoken it.
19 Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
And they shall possesse the South side of the mount of Esau, and the plaine of the Philistims: and they shall possesse the fieldes of Ephraim, and the fieldes of Samaria, and Beniamin shall haue Gilead.
20 Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
And the captiuitie of this host of the children of Israel, which were among the Canaanites, shall possesse vnto Zarephath, and the captiuitie of Ierusalem, which is in Sepharad, shall possesse the cities of the South.
21 Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.
And they that shall saue, shall come vp to mount Zion to iudge the mount of Esau, and the kingdome shalbe the Lords.

< Obadiya 1 >