< Obadiya 1 >

1 Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
Obadiah ni a hmu e kamnuenae: Bawipa Jehovah ni Edom ram hanelah a dei e lawk teh, BAWIPA e hram lawk teh maimouh ni thai awh toe. Nangmouh thaw awh nateh Edom ram tuk hanelah cet awh leih titeh Jentelnaw koe laicei a patoun toe.
2 “Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
Nang teh Jentelnaw e hmalah kathoengca lah na ta, Jentelnaw ni na hnephnap awh han.
3 Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
Talungnaw rahak vah na o teh, kai hah apini nama talai na ka pabawt thai han vâ na ti dawkvah na kâoupnae ni na dum toe.
4 Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
Nang teh langta patetlah na kâtawm teh âsinaw dawk tabu na ka tuk nakunghai, hote hmuen koehoi kai ni nang hah na pabo han telah BAWIPA ni a ti.
5 “In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
Tamrunaw hoi dingcanaw ni karum vah tho awh pawiteh, amamouh ngai e duengdoeh parawt awh tih. Misur paw ka khi e ni hai youn touh teh ouk a pâhma nahoehmaw.
6 Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
Nang teh puenghoi na kamko toe. Esaw teh puenghoi akungkhei awh toe. A hro e hnonaw teh ngit a pâphue awh toe.
7 Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
Nang hoi kamyawng e naw pueng teh ram alawilah pâlei lah ao awh toe. Na huinaw pueng ni na dum awh toe. Nang hoi rei kacatnetnaw ni, nang hanelah tangkam a patung awh toe. Na thoumnae abaw toe.
8 “A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
BAWIPA ni a dei e teh hatnae hnin dawkvah Edom ram thung e lungkaangnaw thoseh, Esaw e mon dawk hoi a ratho kahawinaw thoseh ka takhoe han.
9 Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
Oe Teman kho, na ransanaw ni a taki awh han. Esaw e mon dawk tami pueng a thei awh han.
10 Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
Nang teh na nawngha Jakop na theinae, thama lah na sak e yon kecu dawkvah, yeirai na phawt vaiteh nang teh khoeroe takhoe lah na o han.
11 A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
Nang teh avanglah na onae hnin, ramlouknaw ni nange thaw katawkkungnaw mannae hnin, alouke miphunnaw ni ahnie khopui longkha thung a kâen teh Jerusalem khopui hah cungpam rayunae hnin nah nang teh dâw e tami lah na o.
12 Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
Na nawngha teh ramlouk e tami lah a onae tueng nah laplap na khet kawi na hoeh. Judahnaw rawknae a kâhmo nah na kâoup sin mahoeh. Runae a kâhmo navah, dudamnae lawk na dei kawi nahoeh.
13 Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
Ka taminaw runae a kâhmo nah, a longkha thung kâen kawi na hoeh, a roedeng nah laplap khet kawi na hoeh, a hnopai hai lawp kawi na hoeh.
14 Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
Kahlout e taminaw ngang hanlah lamkâcunae koe kangdue kawi na hoeh. Runae a kâhmo nah a tarannaw kut dawk thak kawi na hoeh.
15 “Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
Bangkongtetpawiteh, BAWIPA e hnin teh miphun pueng hoi a hnai toe. Na sak e patetlah ayâ ni nang koe a sak van han. Na sak e hno na lû van a pha han.
16 Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
Judah miphunnaw ni, kaie mon kathoung dawk a canei e patetlah tengpam kaawm e miphunnaw pueng ni a canei awh han. A canei awh vaiteh a padoun awh toteh kaawm boihoeh e tami patetlah ao han.
17 Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
Zion mon dawk ka hlout e youn touh ao han. Thoungnae hmuen lah ao han. Jakop miphun ni a coe han kamcu e talai bout a coe awh han.
18 Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
Jakop miphun teh hmai, Joseph miphun teh hmaito, Esaw miphun teh songnawng lah ao. Hmai hoi sawi toteh be a kak awh han. Esaw miphun hlout awh mahoeh telah BAWIPA ni a dei toe.
19 Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
Akalah kaawm e naw ni Esaw e mon hai thoseh, tanghling dawk kaawm e naw ni Filistin ram hai thoseh, Ephraim yawn hoi samaria ram hai thoseh, Benjamin miphun ni Gilead ram hai thoseh a tuk han.
20 Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
Kanaannaw koe kaawm e, man e Isarel miphunnaw ni Zarephath totouh a coe awh han. Jerusalem hoi san lah a man awh teh Sepharad ram kaawm e naw ni akalae ram totouh a coe awh han.
21 Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.
Esaw e mon lawkceng hanelah rungngangkungnaw teh, Zion mon dawk a luen awh han. A uknaeram haiyah BAWIPA e ram lah ao han.

< Obadiya 1 >