< Ƙidaya 1 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
Et le Seigneur parla à Moïse dans le désert de Sinaï, dans le tabernacle d’alliance, au premier jour du second mois, à la seconde année de leur sortie d’Égypte, disant:
2 “Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
Faites le dénombrement de toute l’assemblée des enfants d’Israël, selon leur parenté, leurs maisons, et les noms de chacun, de tout ce qui est du sexe masculin,
3 Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
Depuis vingt ans et au-dessus, de tous les hommes forts d’Israël, et vous les dénombrerez, selon leurs bandes, toi et Aaron.
4 Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
Et il y aura avec vous les princes de leurs tribus et de leurs maisons dans leur parenté.
5 “Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
Ceux dont voici les noms: De Ruben, Elisur, fils de Sédéur;
6 daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
De Siméon, Salamiel, fils de Surisaddaï;
7 daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
De Juda, Nahasson, fils d’Aminadab;
8 daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
D’Issachar, Nathanaël, fils de Suar;
9 daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
De Zabulon, Eliab, fils d’Hélon.
10 daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
Et d’entre les fils de Joseph: d’Ephraïm, Elisama, fils d’Amiud; de Manassé, Gamaliel, fils de Phadassur;
11 daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
De Benjamin, Abidan, fils de Gédéon;
12 daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
De Dan, Ahiézer, fils d’Amisaddaï;
13 daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
D’Aser, Phégiel, fils d’Ochran;
14 daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
De Gad, Eliasaph, fils de Duel;
15 daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
De Nephtah, Ahira, fils d’Enan.
16 Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
C’étaient là les plus nobles princes de la multitude selon leurs tribus et leur parenté, et les chefs de l’armée d’Israël,
17 Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
Que prirent Moïse et Aaron avec toute la multitude du peuple,
18 suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
Et qu’ils assemblèrent au premier jour du second mois, les recensant selon la parenté, les maisons, les familles, la personne et le nom de chacun, depuis vingt ans et au-dessus,
19 yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
Comme avait ordonné le Seigneur à Moïse. Or, il y eut de dénombré dans le désert de Sinaï,
20 Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
De Ruben, premier-né d’Israël, selon les générations, les familles, les maisons et le nom de chacun, tout ce qui est du sexe masculin, depuis vingt ans et au-dessus, allant à la guerre,
21 Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
Quarante-six mille cinq cents.
22 Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants de Siméon, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, furent recensés selon le nom et la personne de chacun, tout ce qui est du sexe masculin, depuis vingt ans et au-dessus, allant à la guerre,
23 Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
Cinquante-neuf mille trois cents.
24 Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants de Gad, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, furent recensés selon le nom de chacun depuis vingt ans et au-dessus, comme pouvant tous aller aux combats,
25 Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
Quarante-cinq mille six cent cinquante.
26 Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants de Juda, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, selon le nom de chacun depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats,
27 Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
Furent recensés soixante-quatorze mille six cents.
28 Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants d’Issachar, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, selon le nom de chacun, depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats.
29 Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
Furent recensés cinquante-quatre mille quatre cents.
30 Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants de Zabulon, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, furent recensés selon le nom de chacun, depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats,
31 Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
Cinquante-sept mille quatre cents.
32 Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants de Joseph, enfants d’Ephraïm, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté furent recensés, selon le nom de chacun, depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats,
33 Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
Quarante mille cinq cents.
34 Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Ensuite, des enfants de Manassé selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, furent recensés selon le nom de chacun depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats,
35 Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
Trente-deux mille deux cents.
36 Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des fils de Benjamin, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, furent recensés par le nom de chacun, depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats,
37 Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
Trente-cinq mille quatre cents.
38 Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants de Dan, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, furent recensés par le nom de chacun, depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats,
39 Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
Soixante-deux mille sept cents.
40 Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants d’Aser, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, furent recensés selon les noms de chacun, depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats,
41 Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
Quarante-un mille et cinq cents.
42 Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
Des enfants de Nephthali, selon les générations, les familles et les maisons de leur parenté, furent recensés par les noms de chacun depuis vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller aux combats,
43 Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
Cinquante-trois mille quatre cents.
44 Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
Tels sont ceux que dénombrèrent Moïse, Aaron, et les douze princes d’Israël, chacun selon les maisons de sa parenté.
45 Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
Ainsi le nombre total des enfants d’Israël selon leurs maisons et leurs familles, depuis vingt ans et au-dessus, qui pouvaient aller aux combats, fut
46 Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
De six cent trois mille cinq cent cinquante hommes.
47 Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
Pour les Lévites, ils ne furent pas dénombrés dans la tribu de leurs familles avec eux.
48 Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
Car le Seigneur parla à Moïse, disant:
49 “Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
Ne compte point la tribu de Lévi, et tu ne comprendras point le nombre des Lévites avec les enfants d’Israël:
50 A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
Mais prépose-les au tabernacle du témoignage, à tous ses vases et à tout ce qui appartient aux cérémonies. Eux-mêmes porteront le tabernacle et tous ses ustensiles: ils seront dans le ministère, et c’est autour du tabernacle qu’ils camperont.
51 Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
Lorsqu’il faudra partir, les Lévites enlèveront le tabernacle; lorsqu’il faudra camper, ils le dresseront; tout étranger qui en approchera, sera mis à mort.
52 Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
Mais les enfants d’Israël poseront leur camp, chacun selon ses bandes, ses corps et son armée.
53 Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
Et les Lévites planteront leurs tentes autour du tabernacle, afin que l’indignation ne vienne pas sur les enfants d’Israël, et ils veilleront à la garde du tabernacle du témoignage.
54 Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Les enfants d’Israël firent donc selon tout ce qu’avait ordonné le Seigneur à Moïse.

< Ƙidaya 1 >