< Ƙidaya 9 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
İsrailliler'in Mısır'dan çıkışlarının ikinci yılının birinci ayında RAB Sina Çölü'nde Musa'ya şöyle seslendi:
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
“İsrailliler Fısıh kurbanını belirlenen zamanda kessinler.
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
Bütün kurallar, ilkeler uyarınca kurbanı belirlenen zamanda, bu ayın on dördüncü gününün akşamüstü keseceksiniz.”
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
Böylece Musa İsrailliler'e Fısıh kurbanını kesmelerini söyledi.
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Onlar da Sina Çölü'nde birinci ayın on dördüncü gününün akşamüstü Fısıh kurbanını kestiler. Her şeyi RAB'bin Musa'ya buyurduğu gibi yaptılar.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
Ancak, ölüye dokunduklarından kirli sayılan bazı kişiler o gün Fısıh kurbanını kesemediler. Aynı gün Musa'yla Harun'a gelip
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
Musa'ya, “Ölüye dokunduğumuzdan kirli sayılırız” dediler, “Ama öbür İsrailliler'le birlikte belirlenen zamanda RAB'bin sunusunu sunmamız neden engellensin?”
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
Musa, “RAB'bin sizinle ilgili bana neler söyleyeceğini duyuncaya dek bekleyin” dedi.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
RAB Musa'ya şöyle dedi:
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
“İsrailliler'e de ki, ‘Sizlerden ya da soyunuzdan ölüye dokunduğu için kirli sayılan ya da uzak bir yolculukta bulunan biri RAB'bin Fısıh kurbanını kesebilir.
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
İkinci ayın on dördüncü gününün akşamüstü Fısıh kurbanını kesip mayasız ekmek ve acı otlarla yiyecek.
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
Sabaha dek kurbandan bir şey bırakmayacak, kemiklerini kırmayacak. Fısıh kurbanını bütün kuralları uyarınca kesmelidir.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
Ancak, temiz sayılan ve yolculukta olmayan biri Fısıh kurbanını kesmeyi savsaklarsa, halkının arasından atılacaktır. Çünkü belirlenen zamanda RAB'bin sunusunu sunmamıştır. Günahının cezasını çekecektir.
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
“‘Aranızda yaşayan bir yabancı RAB'bin Fısıh kurbanını kesmek isterse, Fısıh'ın kuralları, ilkeleri uyarınca kesmelidir. Yerli ya da yabancı için aynı kuralı uygulamalısınız.’”
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
Konut, yani Levha Sandığı'nın bulunduğu çadır kurulduğu gün üstünü bulut kapladı. Konutun üstündeki bulut akşamdan sabaha dek ateşi andırdı.
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
Bu hep böyle sürüp gitti. Konutu kaplayan bulut gece ateşi andırıyordu.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
İsrailliler ancak bulut çadırın üzerinden kalkınca göçer, bulut nerede durursa orada konaklarlardı.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
RAB'bin buyruğu uyarınca göç eder, yine RAB'bin buyruğu uyarınca konaklarlardı. Bulut konutun üzerinde durdukça yerlerinden ayrılmazlardı.
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
Bulut konutun üzerinde uzun süre durduğu zaman RAB'bin buyruğuna uyar, yola çıkmazlardı.
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
Bazen bulut konutun üzerinde birkaç gün kalırdı. Halk da RAB'bin verdiği buyruğa göre ya konakladığı yerde kalır ya da göç ederdi.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
Bazı günler bulut akşamdan sabaha dek kalır, sabah konutun üzerinden kalkar kalkmaz halk yola çıkardı. Gece olsun, gündüz olsun, bulut konutun üzerinden kalkar kalkmaz halk yola çıkardı.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
Bulut konutun üzerinde iki gün, bir ay ya da uzun süre kalsa bile, İsrailliler konakladıkları yerde kalır, yola koyulmazlardı. Ama bulut kalkar kalkmaz yola çıkarlardı.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
RAB'bin buyruğu uyarınca konaklar ya da yola çıkarlardı. Böylece RAB'bin Musa aracılığıyla verdiği buyruğa uydular.

< Ƙidaya 9 >