< Ƙidaya 9 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
Og Herren talte til Moses i Sinai ørken i det annet år efterat de var gått ut av Egyptens land, i den første måned, og sa:
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
Israels barn skal holde påske på den fastsatte tid.
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
Den fjortende dag i denne måned, mellem de to aftenstunder, skal I holde påske på den fastsatte tid. Efter alle lover og forskrifter som gjelder om den, skal I holde den.
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
Da talte Moses til Israels barn og sa at de skulde holde påske.
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Og de holdt påske i den første måned, på den fjortende dag i måneden, mellem de to aftenstunder, i Sinai ørken; aldeles som Herren hadde befalt Moses, således gjorde Israels barn.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
Men det var nogen menn som var blitt urene av et lik, så de ikke kunde holde påske den dag; disse menn trådte samme dag frem for Moses og Aron
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
og sa til ham: Vi er blitt urene av et lik; hvorfor skal det være oss nektet å bære frem Herrens offer på den fastsatte tid sammen med de andre Israels barn?
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
Da sa Moses til dem: Vent, så jeg kan få høre hvad Herren befaler om eder.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talte til Moses og sa:
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
Tal til Israels barn og si: Om nogen blandt eder eller blandt eders efterkommere er blitt uren av et lik eller er på langreise, skal han allikevel holde påske for Herren;
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
i den annen måned på den fjortende dag, mellem de to aftenstunder, skal de holde den; med usyret brød og bitre urter skal de ete påskelammet.
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
De skal ikke levne noget av det til om morgenen og ikke bryte noget ben på det; de skal i ett og alt holde påsken efter loven som gjelder om den.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
Men den som er ren og ikke er på reise og enda lar være å holde påske, han skal utryddes av sitt folk, fordi han ikke bar frem Herrens offer på den fastsatte tid; den mann skal lide for sin synd.
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
Og når en fremmed opholder sig hos eder og vil holde påske for Herren, så skal han holde den efter loven om påsken og efter forskriftene om den; der skal gjelde én lov for eder, både for den fremmede og for den innfødte i landet.
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
Den dag tabernaklet blev reist, dekket skyen tabernaklet, vidnesbyrdets telt; og om aftenen var der som et ildskjær over tabernaklet like til om morgenen.
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
Således var det alltid: Skyen dekket det, og om natten var der som et ildskjær.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
Og hver gang skyen løftet sig fra teltet, brøt Israels barn straks op; og på det sted hvor skyen lot sig ned, der leiret Israels barn sig.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
Efter Herrens befaling brøt Israels barn op, og efter Herrens befaling leiret de sig; alle de dager skyen hvilte over tabernaklet, lå de i leir.
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
Når skyen blev over tabernaklet i mange dager, da rettet Israels barn sig efter det som Herren hadde sagt, og brøt ikke op.
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
Stundom hendte det at skyen var bare nogen få dager over tabernaklet; efter Herrens befaling lå de da i leir, og efter Herrens befaling brøt de op.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
Men stundom hendte det at skyen var der bare fra aften til morgen; når da skyen løftet sig om morgenen, brøt de op. Eller den var der en dag og en natt; når da skyen løftet sig, brøt de op.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
Eller den var der et par dager eller en måned eller enda lenger; når skyen drygde så lenge og blev liggende over tabernaklet, da lå Israels barn i leir og brøt ikke op, men når den løftet sig, brøt de op.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
Efter Herrens befaling leiret de sig, og efter Herrens befaling brøt de op; de rettet sig efter det som Herren hadde sagt - efter det som Herren hadde befalt ved Moses.

< Ƙidaya 9 >