< Ƙidaya 9 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
Le Seigneur parla à Moïse dans le désert de Sinaï, à la seconde année après qu’ils furent sortis de la terre d’Egypte, au premier mois, disant:
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
Que les enfants d’Israël fassent la Pâque en son temps,
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
Au quatorzième jour de ce mois, vers le soir, selon toutes ses cérémonies et ses ordonnances.
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
Et Moïse ordonna aux enfants d’Israël qu’ils feraient la Pâque.
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Ils la firent en son temps, au quatorzième jour du mois, sur la montagne de Sinaï. Les enfants d’Israël firent selon tout ce qu’avait commandé le Seigneur à Moïse.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
Or voici que quelques-uns, impurs à cause de l’âme d’un homme, et qui ne pouvaient faire la Pâque en ce jour-là, s’approchant de Moïse et d’Aaron,
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
Leur dirent: Nous sommes impurs à cause de l’âme d’un homme: pourquoi sommes-nous frustrés de pouvoir offrir l’offrande au Seigneur en son temps parmi les enfants d’Israël?
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
Moïse leur répondit: Attendez que je consulte le Seigneur sur ce qu’il ordonnera de vous.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Et le Seigneur parla à Moïse, disant:
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
Dis aux enfants d’Israël: Qu’un homme dans votre nation qui sera impur à cause d’une âme, ou en voyage au loin, fasse la Pâque du Seigneur
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
Au second mois, au quatorzième jour du mois, vers le soir; c’est avec des azymes et des laitues sauvages qu’il la mangera;
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
Il n’en laissera rien jusque au matin et il n’en rompra point les os: il observera tout le rite de la Pâque.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
Mais si quelqu’un est même pur, et n’est point en voyage, et que cependant il ne fasse point la Pâque, cette âme sera exterminée du milieu de ses peuples; parce qu’il n’a pas offert de sacrifice au Seigneur en son temps: il portera lui-même son péché.
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
Un voyageur aussi et un étranger, s’ils se trouvent chez vous, feront la Pâque du Seigneur selon ses cérémonies et ses ordonnances. Ce sera un précepte parmi vous, tant pour l’étranger que pour l’indigène.
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
Donc au jour que fut dressé le tabernacle, la nuée le couvrit. Mais depuis le soir, il y eut sur la tente comme une espèce de feu jusqu’au matin.
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
Ainsi arrivait-il toujours: pendant le jour la nuée couvrait le tabernacle, et pendant la nuit, comme une espèce de feu.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
Et lorsque la nuée qui couvrait le tabernacle était enlevée, les enfants d’Israël partaient; et dans le lieu où elle s’arrêtait, là ils campaient.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
Au commandement du Seigneur ils partaient, et à son commandement ils dressaient le tabernacle. Pendant tous les jours que la nuée se tenait sur le tabernacle, ils demeuraient dans le même lieu.
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
Et s’il arrivait qu’elle demeurât longtemps sur lui, les enfants d’Israël étaient en observation du Seigneur, et partaient pas,
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
Autant de jours que la nuée était sur le tabernacle. Au commandement du Seigneur, ils dressaient les tentes, et à son commandement, ils les enlevaient.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
Si la nuée restait depuis le soir jusqu’au matin, et qu’aussitôt le point du jour elle quittât le tabernacle, ils partaient: et si après un jour et une nuit elle se retirait, ils détendaient les tentes.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
Mais si elle était deux jours, ou un mois ou plus longtemps sur le tabernacle, les enfants d’Israël demeuraient dans le même lieu et ne partaient pas; mais dès qu’elle s’était retirée, ils levaient le camp.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
C’était sur la parole du Seigneur qu’ils plantaient les tentes, et sur sa parole qu’ils partaient: et ils étaient en observation du Seigneur, selon son commandement par l’entremise de Moïse.

< Ƙidaya 9 >