< Ƙidaya 9 >
1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
Yahvé parla à Moïse dans le désert de Sinaï, le premier mois de la deuxième année après leur sortie du pays d'Égypte, et dit:
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
« Que les enfants d'Israël célèbrent la Pâque au temps fixé.
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
Le quatorzième jour de ce mois, au soir, vous la célébrerez au temps fixé. Vous la célébrerez selon toutes ses lois et selon toutes ses ordonnances. »
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
Moïse dit aux enfants d'Israël qu'ils devaient célébrer la Pâque.
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Ils célébrèrent la Pâque au premier mois, le quatorzième jour du mois, au soir, dans le désert du Sinaï. Les enfants d'Israël firent tout ce que Yahvé avait ordonné à Moïse.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
Il y avait des hommes qui étaient impurs à cause d'un cadavre d'homme, de sorte qu'ils ne pouvaient pas célébrer la Pâque ce jour-là, et ils se présentèrent devant Moïse et Aaron ce jour-là.
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
Ces hommes lui dirent: « Nous sommes impurs à cause du cadavre d'un homme. Pourquoi sommes-nous retenus, afin de ne pas offrir l'offrande de Yahvé au temps fixé parmi les enfants d'Israël? »
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
Moïse leur répondit: « Attendez, afin que j'entende ce que l'Éternel commandera à votre sujet. »
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse, et dit:
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
Dis aux enfants d'Israël: « Si l'un d'entre vous ou l'un de vos descendants est impur à cause d'un cadavre, ou s'il est en voyage lointain, il célébrera quand même la Pâque en l'honneur de Yahvé.
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
Au deuxième mois, le quatorzième jour, au soir, ils la célébreront; ils la mangeront avec des pains sans levain et des herbes amères.
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
Ils n'en laisseront rien jusqu'au matin, et ils n'en briseront pas un os. Ils observeront toutes les règles de la Pâque.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
Mais l'homme qui est pur, qui n'est pas en voyage, et qui ne célèbre pas la Pâque, cette personne sera retranchée de son peuple. Parce qu'il n'a pas offert l'offrande de Yahvé au temps fixé, cet homme portera son péché.
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
"'Si un étranger habite parmi vous et désire célébrer la Pâque en l'honneur de Yahvé, il le fera selon le statut de la Pâque et selon son ordonnance. Vous aurez un seul statut, tant pour l'étranger que pour celui qui est né dans le pays. »"
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
Le jour où le tabernacle fut élevé, la nuée couvrit le tabernacle, la Tente du Témoignage. Le soir, elle était au-dessus du tabernacle, comme une apparence de feu, jusqu'au matin.
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
Il en était ainsi continuellement. La nuée le couvrait, et l'aspect du feu pendant la nuit.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
Chaque fois que la nuée s'éloignait de la Tente, les enfants d'Israël partaient; et les enfants d'Israël campaient à l'endroit où la nuée restait.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
Sur l'ordre de l'Éternel, les enfants d'Israël partirent, et ils campèrent sur l'ordre de l'Éternel. Tant que la nuée resta sur le tabernacle, ils restèrent campés.
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
Lorsque la nuée restait plusieurs jours sur le tabernacle, les enfants d'Israël respectaient l'ordre de l'Éternel et ne voyageaient pas.
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
Parfois, la nuée restait quelques jours sur la tente; alors, selon le commandement de l'Éternel, ils restaient campés, et selon le commandement de l'Éternel, ils voyageaient.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
Parfois la nuée était du soir jusqu'au matin; et quand la nuée se levait le matin, ils voyageaient; ou bien, de jour et de nuit, quand la nuée se levait, ils voyageaient.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
Que la nuée soit restée sur le tabernacle pendant deux jours, un mois ou un an, les enfants d'Israël restaient campés et ne voyageaient pas; mais quand elle était levée, ils voyageaient.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
Sur l'ordre de Yahvé, ils campaient, et sur l'ordre de Yahvé, ils voyageaient. Ils ont observé l'ordre de Yahvé, sur l'ordre de Yahvé donné par Moïse.