< Ƙidaya 9 >
1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
One year after the Israelis left Egypt, during the month of March, while they were in the Sinai Desert, Yahweh said to Moses/me,
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
“Tell the Israeli people that they must celebrate the Passover [Festival again].
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
They must do it on the fourteenth day of this month, early in the evening, and they must obey all the instructions about it [that I gave you previously].”
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
So Moses/I told the people what Yahweh had said about celebrating the Passover.
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
The people celebrated it, there in the Sinai Desert, in the evening of the fourteenth day of the month, just as Yahweh had commanded Moses/me.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
But some of the Israeli people had touched a corpse, and as a result they had become unfit to celebrate the Passover. So they asked Aaron and Moses/me,
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
“It is true that we have touched a corpse. But why should that prevent us from celebrating the Passover Festival and offering sacrifices to Yahweh like everyone else [RHQ]?”
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
Moses/I replied, “Wait here until I go into the Sacred Tent and find out what Yahweh says about it.”
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
[So Moses/I went into the tent and asked Yahweh what he/I should tell the people], and this is what Yahweh said:
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
“Tell this to the Israeli people: If any of you or your descendants touch a corpse and as a result become unacceptable to me, or if you are away from home on a long trip [at the time to celebrate the Passover], you will still be permitted to celebrate it.
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
But you must celebrate it exactly one month later, early in the evening of the fourteenth day of that month. Eat the meat of the lamb for the Passover Festival with bread that is baked without yeast and eat bitter herbs.
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
Do not leave any of it until the next morning. And do not break any of the lamb’s bones. Obey all the regulations about celebrating the Passover.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
But if any of you has not done anything that would make you unfit to celebrate the Passover Festival, and you are not away from home on a long trip, and you do not sacrifice to me at the proper time, you will no longer be allowed to associate with my people. (You will be punished/I will punish you).
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
Foreigners who live among you may also celebrate the Passover Festival, if they obey all my commands concerning it.”
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
On the day that the Sacred Tent was set up, a cloud covered it. From the time that the sun set until the time that the sun rose [the next day], the cloud resembled a [huge] fire. And that is what happened every day [that we/the Israelis were in the desert].
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
When the cloud rose up and started to move [to a new location], we/they followed it. When the cloud stopped, we/the Israelis stopped there and set up their tents.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
We/They traveled when Yahweh, [by causing the cloud to move or stop], signaled to us/them when to move and when to stop. When the cloud stayed over the Sacred Tent, we/the Israelis stayed at that place.
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
Sometimes the cloud stayed over the tent for a long time, so when that happened, we/they did not travel.
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
Sometimes the cloud remained over the tent for only a few days. We/The people stopped and set up our/their tents as Yahweh commanded us/them, and we/they traveled [to a new location] when Yahweh commanded us/them to do that.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
Sometimes the cloud stayed in one place for only one day. When that happened, when the cloud rose up [into the sky] the next morning, then we/they traveled. Whenever the cloud moved, during the day or during the night, we/they traveled.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
If the cloud stayed over the Sacred Tent for two days, or for a month, or for a year, during that time we/they stayed where we/they were. But when the cloud rose up [into the sky], we/they started to travel.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
When Yahweh commanded us/them to [stop and] set up our/their tents, we/they did that. When he told us/them to move, we/they moved. We/They did whatever Yahweh told Moses/me that we/they should do.