< Ƙidaya 9 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
The Lord spoke to Moses in the desert of Sinai, the second year after they were come out of the land of Egypt, in the first month, saying:
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
Let the children of Israel make the phase in its due time,
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
The fourteenth day of this month in the evening, according to all the ceremonies and justifications thereof.
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
And Moses commanded the children of Israel that they should make the phase.
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And they made it in its proper time: the fourteenth day of the month at evening, in mount Sinai. The children of Israel did according to all things that the Lord had commanded Moses.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
But behold some who were unclean by occasion of the soul of a man, who could not make the phase on that day, coming to Moses and Aaron,
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
Said to them: We are unclean by occasion of the soul of a man. Why are we kept back that we may not offer in its season the offering to the Lord among the children of Israel?
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
And Moses answered them: Stay that I may consult the Lord what he will ordain concerning you.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying:
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
Say to the children of Israel: The man that shall be unclean by occasion of one that is dead, or shall be in a journey afar off in your nation, let him make the phase to the Lord.
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
In the second month, on the fourteenth day of the month in the evening, they shall eat it with unleavened bread and wild lettuce:
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
They shall not leave any thing thereof until morning, a nor break a bone thereof, they shall observe all the ceremonies of the phase.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
But if any man is clean, and was not on a journey, and did not make the phase, that soul shall be cut off from among his people, because he offered not sacrifice to the Lord in due season: he shall bear his sin.
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
The sojourner also and the stranger if they be among you, shall make the phase to the Lord according to the ceremonies and justifications thereof. The same ordinance shall be with you both for the stranger, and for him that was born in the land.
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
Now on the day that the tabernacle was reared up, a cloud covered it. But from the evening there was over the tabernacle, as it were, the appearance of fire until the morning.
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
So it was always: by day the cloud covered it, and by night as it were the appearance of fire.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
And when the cloud that covered the tabernacle was taken up, then the children of Israel marched forward: and in the place where the cloud stood still, there they camped.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
At the commandment of the Lord they marched, and at his commandment they pitched the tabernacle. All the days that the cloud abode over the tabernacle, they remained in the same place:
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
And if it was so that it continued over it a long time, the children of Israel kept the watches of the Lord, and marched not,
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
For as many days soever as the cloud stayed over the tabernacle. At the commandment of the Lord they pitched their tents, and at his commandment they took them down.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
If the cloud tarried from evening until morning, and immediately at break of day left the tabernacle, they marched forward: and if it departed after a day and a night, they took down their tents.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
But if it remained over the tabernacle for two days or a month or a longer time, the children of Israel remained in the same place, and marched not: but immediately as soon as it departed, they removed the camp.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
By the word of the Lord they pitched their tents, and by his word they marched: and kept the watches of the Lord according to his commandment by the hand of Moses.

< Ƙidaya 9 >