< Ƙidaya 9 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
And Jehovah spoke to Moses in the wilderness of Sinai, in the first month of the second year after they came out of the land of Egypt, saying,
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
Moreover let the sons of Israel keep the Passover in its appointed season.
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
In the fourteenth day of this month, at evening, ye shall keep it in its appointed season. According to all the statutes of it, and according to all the ordinances of it, ye shall keep it.
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
And Moses spoke to the sons of Israel, that they should keep the Passover.
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And they kept the Passover in the first month, on the fourteenth day of the month, at evening, in the wilderness of Sinai. According to all that Jehovah commanded Moses, so did the sons of Israel.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
And there were certain men who were unclean by reason of the dead body of a man, so that they could not keep the Passover on that day. And they came before Moses and before Aaron on that day,
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
and those men said to him, We are unclean by reason of the dead body of a man. Why are we kept back, that we may not offer the oblation of Jehovah in its appointed season among the sons of Israel?
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
And Moses said to them, Stay ye, that I may hear what Jehovah will command concerning you.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
Speak to the sons of Israel, saying, If any man of you or of your generations shall be unclean by reason of a dead body, or be on a journey afar off, yet he shall keep the Passover to Jehovah.
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
In the second month on the fourteenth day at evening they shall keep it. They shall eat it with unleavened bread and bitter herbs.
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
They shall leave none of it to the morning, nor break a bone of it. According to all the statute of the Passover they shall keep it.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
But the man who is clean, and is not on a journey, and forbears to keep the Passover, that soul shall be cut off from his people, because he did not offer the oblation of Jehovah in its appointed season; that man shall bear his sin.
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
And if a stranger shall sojourn among you, and will keep the Passover to Jehovah, according to the statute of the Passover, and according to the ordinance of it, so shall he do. Ye shall have one statute, both for the sojourner, and for him who is born in the land.
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
And on the day that the tabernacle was reared up the cloud covered the tabernacle, even the tent of the testimony, and at evening it was upon the tabernacle, as it were the appearance of fire, until morning.
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
So it was always: the cloud covered it, and the appearance of fire by night.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
And whenever the cloud was taken up from over the tent, then after that the sons of Israel journeyed. And in the place where the cloud abode, there the sons of Israel encamped.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
At the commandment of Jehovah the sons of Israel journeyed, and at the commandment of Jehovah they encamped. As long as the cloud abode upon the tabernacle they remained encamped.
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
And when the cloud tarried upon the tabernacle many days, then the sons of Israel kept the charge of Jehovah, and did not journey.
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
And sometimes the cloud was a few days upon the tabernacle, then according to the commandment of Jehovah they remained encamped, and according to the commandment of Jehovah they journeyed.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
And sometimes the cloud was from evening until morning, and when the cloud was taken up in the morning, they journeyed, or if by day and by night, when the cloud was taken up, they journeyed.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
Whether it was two days, or a month, or a year, that the cloud tarried upon the tabernacle, abiding on it, the sons of Israel remained encamped, and did not journey, but when it was taken up, they journeyed.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
At the commandment of Jehovah they encamped, and at the commandment of Jehovah they journeyed. They kept the charge of Jehovah, at the commandment of Jehovah by Moses.

< Ƙidaya 9 >