< Ƙidaya 9 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
HERREN talede saaledes til Moses i Sinaj Ørken i den første Maaned af det andet Aar efter deres Udvandring fra Ægypten:
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
Israeliterne skal fejre Paasken til den fastsatte Tid,
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
paa den fjortende Dag i denne Maaned ved Aftenstid skal I fejre den til den fastsatte Tid; overensstemmende med alle Anordningerne og Lovbudene om den skal I fejre den!
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
Da sagde Moses til Israeliterne, at de skulde fejre Paasken;
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
og de fejrede Paasken i Sinaj Ørken den fjortende Dag i den første Maaned ved Aftenstid; nøjagtigt som HERREN havde paalagt Moses, saaledes gjorde Israeliterne.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
Men der var nogle Mænd, som var blevet urene ved et Lig og derfor ikke kunde fejre Paaske den Dag. Disse Mænd traadte nu den Dag frem for Moses og Aron
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
og sagde til ham: »Vi er blevet urene ved et Lig; hvorfor skal det da være os forment at frembære HERRENS Offergave til den fastsatte Tid sammen med de andre Israeliter?«
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
Moses svarede dem: »Vent, til jeg faar at høre, hvad HERREN paabyder angaaende eder!«
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Da talede HERREN til Moses og sagde:
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
Tal til Israeliterne og sig: Naar nogen af eder eller eders Efterkommere er blevet uren ved et Lig eller er ude paa en lang Rejse, skal han alligevel holde Paaske for HERREN;
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
den fjortende Dag i den anden Maaned ved Aftenstid skal de holde den; med usyret Brød og bitre Urter skal de spise Paaskelammet.
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
De maa intet levne deraf til næste Morgen, og de maa ikke sønderbryde noget af dets Ben. De skal fejre Paasken i Overensstemmelse med alle de Anordninger, som gælder for den.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
Men den, som undlader at fejre Paasken, skønt han er ren og ikke paa Rejse, det Menneske skal udryddes af sin Slægt, fordi han ikke har frembaaret HERRENS Offergave til den fastsatte Tid. Den Mand skal undgælde for sin Synd.
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
Og naar en fremmed, der bor hos eder, vil holde Paaske for HERREN, skal han holde den efter de Anordninger og Lovbud, som gælder for Paasken. En og samme Lov skal gælde for eder, for den fremmede og for den indfødte.
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
Den Dag Boligen blev rejst, dækkede Skyen Boligen, Vidnesbyrdets Telt; men om Aftenen var der som et Ildskær over Boligen, og det holdt sig til om Morgenen.
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
Saaledes var det til Stadighed: Om Dagen dækkede Skyen den, om Natten Ildskæret.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
Hver Gang Skyen løftede sig fra Teltet, brød Israeliterne op, og der, hvor Skyen stod stille, slog Israeliterne Lejr.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
Paa HERRENS Bud brød Israeliterne op, og paa HERRENS Bud gik de i Lejr, og saa længe Skyen hvilede over Boligen, blev de liggende i Lejr;
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
naar Skyen blev over Boligen i længere Tid, rettede Israeliterne sig efter, hvad HERREN havde foreskrevet dem, og brød ikke op.
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
Det hændte, at Skyen kun blev nogle faa Dage over Boligen; da gik de i Lejr paa HERRENS Bud og brød op paa HERRENS Bud.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
Og det hændte, at Skyen kun blev der fra Aften til Morgen; naar Skyen da løftede sig om Morgenen, brød de op. Eller den blev der en Dag og en Nat; naar Skyen da løftede sig, brød de op.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
Eller den blev der et Par Dage eller en Maaned eller længere endnu, idet Skyen i længere Tid hvilede over Boligen; saa blev Israeliterne liggende i Lejr og brød ikke op, men naar den løftede sig, brød de op.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
Paa HERRENS Bud gik de i Lejr, og paa HERRENS Bud brød de op; de rettede sig efter, hvad HERREN havde foreskrevet dem, efter HERRENS Bud ved Moses.

< Ƙidaya 9 >