< Ƙidaya 8 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
2 “Yi magana da Haruna, ka ce masa, ‘Sa’ad da za ka shisshirya fitilun nan bakwai, ka shirya su yadda za su fuskanci gaba domin haskensu yă haskaka ta gaba.’”
Parle à Aaron et tu lui diras: Lorsque tu auras placé les sept lampes, que le chandelier soit dressé à la partie australe. Ordonne donc que les lampes regardent contre le nord vis-à-vis de la table des pains de proposition; c’est contre cette partie que leurs le chandelier regarde, qu’elles devront luire.
3 Haka kuwa Haruna ya yi; ya shisshirya fitilun yadda za su fuskanci gaba a kan wurin ajiye fitilan, kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Et Aaron le fit, et il posa les lampes sur le chandelier, comme avait ordonné le Seigneur à Moïse.
4 Ga yadda aka yi wurin ajiye fitilan. An ƙera shi da zinariya daga gindinsa har zuwa sama inda ya buɗu. Aka ƙera wurin ajiye fitilan yadda Ubangiji ya nuna wa Musa.
Or voici la façon du chandelier: il était d’or ductile, tant la tige du milieu, que tout ce qui sortait des deux côtés des branches: c’est selon le modèle que montra le Seigneur à Moïse, que Moïse fit le chandelier.
5 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
6 “Keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, ka tsarkake su.
Prends les Lévites du milieu d’Israël, et tu les purifieras
7 Ga yadda za ka tsarkake su, ka yayyafa musu ruwan tsarkakewa; ka sa su aske jikunansu duka su kuma wanke tufafinsu, ta haka za su tsarkake kansu.
Selon ce rite: Qu’ils soient aspergés d’eau de purification, et qu’ils rasent tous les poils de leur chair. Et lorsqu’ils auront lavé leurs vêtements, et qu’ils seront purifiés,
8 Ka sa su ɗauki ɗan bijimi tare da lallausan garin hadaya, kwaɓaɓɓe da mai; sa’an nan, kai kuma ka ɗauki ɗan bijimi na biyu na hadaya don zunubi.
Ils prendront un bœuf des troupeaux, avec sa libation, de la fleur de farine arrosée d’huile: et toi, tu prendras un autre bœuf du troupeau pour le péché;
9 Ka kawo Lawiyawa a gaban Tentin Sujada, ka kuma kira taron Isra’ilawa duka.
Et tu feras approcher les Lévites devant le tabernacle d’alliance, toute la multitude des enfants d’Israël ayant été convoquée.
10 Za ka kawo Lawiyawa a gaban Ubangiji, Isra’ilawa kuma za su ɗibiya musu hannuwansu.
Et lorsque les Lévites seront devant le Seigneur, les enfants d’Israël poseront leurs mains sur eux,
11 Haruna zai miƙa Lawiyawa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa daga Isra’ilawa, saboda a shirya su domin aikin Ubangiji.
Et Aaron offrira les Lévites en la présence du Seigneur, comme un don de la part des enfants d’Israël, afin qu’ils le servent dans son ministère.
12 “Bayan Lawiyawa sun ɗibiya hannuwansu a kan bijiman, sai ka yi amfani da ɗaya a matsayin hadaya don zunubi ga Ubangiji, ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa, don yin kafara saboda Lawiyawa.
Les Lévites aussi poseront leurs mains sur la tête des bœufs, dont tu sacrifieras l’un pour le péché, et l’autre pour l’holocauste du Seigneur, afin que tu pries pour eux.
13 Ka kuma sa Lawiyawa su tsaya a gaban Haruna da’ya’yansa, sai ka miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji.
Tu présenteras ensuite les Lévites devant Aaron et ses fils, et tu les consacreras après les avoir offerts au Seigneur,
14 Da haka za ka keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, Lawiyawa za su zama nawa.
Et tu les sépareras du milieu des enfants d’Israël, afin qu’ils soient à moi;
15 “Bayan ka tsarkake Lawiyawa, ka kuma miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa, sai su zo su yi aikinsu a Tentin Sujada.
Et après cela ils entreront dans le tabernacle d’alliance, pour qu’ils me servent. Et c’est ainsi que tu les purifieras et les consacreras pour l’oblation du Seigneur, parce qu’ils m’ont été donnés en don par les enfants d’Israël.
16 Gama dukansu an ba ni su daga cikin Isra’ilawa a maimakon dukan waɗanda suka fara buɗe mahaifa, wato, dukan’ya’yan farin Isra’ilawa. Na karɓi Lawiyawa su zama nawa.
C’est en place des premiers-nés qui ouvrent un sein quelconque, que je les ai reçus.
17 Kowane ɗan farin haihuwa, ko mutum, ko dabba a Isra’ila, nawa ne. Sa’ad da na kashe’ya’yan fari a Masar, na keɓe’ya’yan fari na Isra’ilawa wa kaina.
Car ils sont à moi, tous les premiers-nés des enfants d’Israël, tant des hommes que des bêtes. Depuis le jour que j’ai frappé tout premier-né dans la terre d’Egypte, je les ai consacrés pour moi;
18 Na kuma ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari maza a Isra’ila.
Et j’ai pris les Lévites au lieu de tous les premiers-nés des enfants d’Israël;
19 Cikin dukan Isra’ilawa, na ba da Lawiyawa kyauta ga Haruna da’ya’yansa, su yi hidima a Tentin Sujada a madadin Isra’ilawa, su kuma yi kafara dominsu saboda kada annoba ta bugi Isra’ilawa sa’ad da suka je kusa da wuri mai tsarki.”
Et j’en ai fait don à Aaron et à ses fils, les tirant du milieu du peuple, pour qu’ils me servent au lieu d’Israël dans le tabernacle d’alliance, et qu’ils prient pour eux, afin qu’il n’y ait pas de plaie sur le peuple, s’il osait approcher du sanctuaire.
20 Musa, Haruna da kuma dukan taron Isra’ilawa, suka yi da Lawiyawa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Or, Moïse et Aaron et toute la multitude des enfants d’Israël firent touchant les Lévites ce qu’avait ordonné le Seigneur à Moïse:
21 Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma wanke tufafinsu. Sai Haruna ya miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa a gaban Ubangiji, ya kuma yi kafara saboda su don yă tsarkake su.
Ils furent donc purifiés, et ils lavèrent leurs vêtements; et Aaron les éleva en la présence du Seigneur, et il pria pour eux,
22 Bayan haka, sai Lawiyawa suka zo don su yi aikinsu a Tentin Sujada, a ƙarƙashin Haruna da’ya’yansa. Suka yi da Lawiyawa kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Afin que purifiés, ils entrassent dans le tabernacle d’alliance pour leurs fonctions devant Aaron et ses fils. Comme le Seigneur avait ordonné à Moïse touchant les Lévites, ainsi il fut lait.
23 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
24 “Wannan ya shafi Lawiyawa ne, wato, mazan da suka kai shekara ashirin da biyar, ko fiye, za su zo su yi aiki a Tentin Sujada,
Voici la loi des Lévites: Depuis vingt-cinq ans et au-dessus, ils entreront pour servir dans le tabernacle d’alliance.
25 amma in suka kai shekaru hamsin da haihuwa, dole su huta daga wannan aiki na yau da kullum, su kuma daina aiki.
Et lorsqu’ils auront accompli la cinquantième année d’âge, ils cesseront de servir,
26 Za su iya taimakon’yan’uwansu cikin tafiyar da ayyuka a Tentin Sujada, amma su kansu ba za su yi aikin ba. Haka fa za ka ba wa Lawiyawa aikinsu.”
Et ils seront les ministres de leurs frères dans le tabernacle d’alliance, pour garder ce qui leur aura été confié; mais les fonctions elles-mêmes, qu’ils ne les fassent point. Tu régleras ainsi pour les Lévites touchant leur garde.

< Ƙidaya 8 >