< Ƙidaya 8 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh said to Moses/me,
2 “Yi magana da Haruna, ka ce masa, ‘Sa’ad da za ka shisshirya fitilun nan bakwai, ka shirya su yadda za su fuskanci gaba domin haskensu yă haskaka ta gaba.’”
“Tell Aaron to put the seven lamps on the lampstand and place them in such a way that they shine toward the front of the lampstand.”
3 Haka kuwa Haruna ya yi; ya shisshirya fitilun yadda za su fuskanci gaba a kan wurin ajiye fitilan, kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
So [Moses/I told him what Yahweh said], and he did that.
4 Ga yadda aka yi wurin ajiye fitilan. An ƙera shi da zinariya daga gindinsa har zuwa sama inda ya buɗu. Aka ƙera wurin ajiye fitilan yadda Ubangiji ya nuna wa Musa.
The lampstand had been made from gold that had been hammered [from one large lump of gold], from its base to the decorations at the top [that resembled] flowers. The lampstand was made exactly like Yahweh had told Moses/me that it should be made.
5 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh also said to Moses/me,
6 “Keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, ka tsarkake su.
“You must cause the descendants of Levi to be acceptable to me by setting them apart from the other Israeli people.
7 Ga yadda za ka tsarkake su, ka yayyafa musu ruwan tsarkakewa; ka sa su aske jikunansu duka su kuma wanke tufafinsu, ta haka za su tsarkake kansu.
Do that by sprinkling them with water [which will symbolize] their being freed/cleansed from [the guilt of] their sins. Then they must shave [off all the hair on] their bodies and wash their clothes.
8 Ka sa su ɗauki ɗan bijimi tare da lallausan garin hadaya, kwaɓaɓɓe da mai; sa’an nan, kai kuma ka ɗauki ɗan bijimi na biyu na hadaya don zunubi.
Then they must bring to the Sacred Tent one bull and some grain mixed with [olive] oil. [Those things will be burned] as sacrifices. They must also bring another bull [that will enable me to forgive them] for the sins they have committed.
9 Ka kawo Lawiyawa a gaban Tentin Sujada, ka kuma kira taron Isra’ilawa duka.
Then you must summon all the Israeli people to come together in front of the Sacred Tent, to [gather around] the descendants of Levi.
10 Za ka kawo Lawiyawa a gaban Ubangiji, Isra’ilawa kuma za su ɗibiya musu hannuwansu.
Then the Israeli people must lay their hands on the descendants of Levi.
11 Haruna zai miƙa Lawiyawa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa daga Isra’ilawa, saboda a shirya su domin aikin Ubangiji.
Aaron must then present them to me to be a gift from the Israeli people, in order that they can work for me [at the Sacred Tent].
12 “Bayan Lawiyawa sun ɗibiya hannuwansu a kan bijiman, sai ka yi amfani da ɗaya a matsayin hadaya don zunubi ga Ubangiji, ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa, don yin kafara saboda Lawiyawa.
“After that, the descendants of Levi must place their hands on the heads of the two bulls. Then the bulls will be [killed and] burned on the altar. One will be an offering to enable me [to forgive them for] sins they have committed, and the other will be completely burned [to please me].
13 Ka kuma sa Lawiyawa su tsaya a gaban Haruna da’ya’yansa, sai ka miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji.
The descendants of Levi must stand [at the altar] in front of Aaron and his sons, and you must then dedicate to me the descendants of Levi.
14 Da haka za ka keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, Lawiyawa za su zama nawa.
This ritual will show that the descendants of Levi are set apart from the other Israelis and that they belong to me.
15 “Bayan ka tsarkake Lawiyawa, ka kuma miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa, sai su zo su yi aikinsu a Tentin Sujada.
“After the descendants of Levi have been made acceptable to me, and presented to me like a special offering, they may start to work at the Sacred Tent.
16 Gama dukansu an ba ni su daga cikin Isra’ilawa a maimakon dukan waɗanda suka fara buɗe mahaifa, wato, dukan’ya’yan farin Isra’ilawa. Na karɓi Lawiyawa su zama nawa.
They will belong to me. They will work for me as substitutes for the firstborn males of all the Israelis, [who also belong to me].
17 Kowane ɗan farin haihuwa, ko mutum, ko dabba a Isra’ila, nawa ne. Sa’ad da na kashe’ya’yan fari a Masar, na keɓe’ya’yan fari na Isra’ilawa wa kaina.
All the firstborn males in Israel, both the people and the animals, are mine. When I caused all the firstborn sons of the people of Egypt to die, [I (spared/did not kill) the firstborn males of the Israelis]. I set them apart to belong to me. I said that the firstborn males of all their domestic animals would also belong to me.
18 Na kuma ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari maza a Isra’ila.
But now I have chosen the descendants of Levi to take the places of the firstborn males of other Israelis.
19 Cikin dukan Isra’ilawa, na ba da Lawiyawa kyauta ga Haruna da’ya’yansa, su yi hidima a Tentin Sujada a madadin Isra’ilawa, su kuma yi kafara dominsu saboda kada annoba ta bugi Isra’ilawa sa’ad da suka je kusa da wuri mai tsarki.”
I have appointed the descendants of Levi to help Aaron and his sons at the Sacred Tent, as Aaron and his sons offer the sacrifices so that the Israeli people’s sins will be forgiven, and to prevent the Israelis from coming close to the tent with the result that a plague would cause many of them to become sick and die.”
20 Musa, Haruna da kuma dukan taron Isra’ilawa, suka yi da Lawiyawa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Aaron and Moses/I and the other Israelis helped the descendants of Levi to do everything that Yahweh had commanded.
21 Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma wanke tufafinsu. Sai Haruna ya miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa a gaban Ubangiji, ya kuma yi kafara saboda su don yă tsarkake su.
The descendants of Levi [sprinkled themselves with water to symbolize that] they had been freed/cleansed from [the guilt of] their sins, and they washed their clothes. Then Aaron brought them to [the altar to] present them to Yahweh, and he offered sacrifices to cleanse them from [the guilt of] their sins and cause them to become acceptable to Yahweh.
22 Bayan haka, sai Lawiyawa suka zo don su yi aikinsu a Tentin Sujada, a ƙarƙashin Haruna da’ya’yansa. Suka yi da Lawiyawa kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
After that, the descendants of Levi started to work at the Sacred Tent to assist Aaron and his sons. They did that just as Yahweh had commanded Moses/me.
23 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh also said this to Moses/me:
24 “Wannan ya shafi Lawiyawa ne, wato, mazan da suka kai shekara ashirin da biyar, ko fiye, za su zo su yi aiki a Tentin Sujada,
“The descendants of Levi who are between 25 and 50 years old will work at the Sacred Tent.
25 amma in suka kai shekaru hamsin da haihuwa, dole su huta daga wannan aiki na yau da kullum, su kuma daina aiki.
But after they become 50 years old, they must (retire/not do that work any more).
26 Za su iya taimakon’yan’uwansu cikin tafiyar da ayyuka a Tentin Sujada, amma su kansu ba za su yi aikin ba. Haka fa za ka ba wa Lawiyawa aikinsu.”
They may help the other descendants of Levi to do their work at the Sacred Tent, but they must not do the work themselves. That is what you must tell them about the work they will do.”

< Ƙidaya 8 >